Connect with us

KANUN LABARAI

Yansanda a Kano sun kama wanda ya sassari matarsa a kotu

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama mutumin da ya sassari matar sa mai dauke da juna biyu tare da wanta a harabar kotu bayan da mai shari’a ya raba auren su a ranar Litinin data gabata.

Kano focus ta ruwaito cewa mai magana da yawun rundunar Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ranar Juma’a a anan Kano.

Kiyawa ya ce an kama Bilyaminu Abdullahi  mai shekara 48 bisa zargin yunkurin kisan kai ta hanyar sarar matar sa Shafa’atu Sale  wanta Ado Sale a harabar kotun shari’ar musulunci dake karamar hukumar Rano.

Da yake jawabi wanda ake zargi Bilyaminu Abdullahi ya ce ya aikata laifin da ake zargin sa akai ne sakamakon hukuncin da alkali ya yanke bai yi masa dadi ba.

“Alkali yace ya raba aure na da ita akan fansar naira dubu ashirin, duk da na fada masa cewa ni matata nake so ba wai kudinne yayimin kadan ba amma ya ce a tura a kwashe kayan ta.

“Abinda ya bata min rai kenan ana fitowa daga kotu na kama yankar su da wuka.

“Wuka tace ina sana’ar saida zuma ne kuma na yanke ta akanta da hannunta shi kuma na yanke shi a kafadarsa da hannun sa,” a cewar Bilyaminu.

Kotu a Kano ta yankewa gawa daurin shekara guda a gidan yari

Miji ya sassari matarsa a gaban kotu a Kano

An kafa kotunan sauraron korafin zaben kananan hukumomi a Kano

Ya kara da cewa wantane ya maida ita gida, da ya bibiya don jin ba’asi sai iyayen  da ‘yan uwanta suka nemi da ya sakar musu ‘yar su.

Ya kuma ce bayan da yaki amincewa ya sake ta ne, suka maka shi kara a gaban kotu da har takai ga alkali ya raba auren su.

A nata bangaren Shafa’atu Sale ta ce duka da cin zarafi ne yasa ta nemi da a raba auren nasu.

Ta kara da cewa bayan da suka fito daga kotune sai ya dinga kiran sunanta, kin amsawar da tayi sai ya zaro wuka ya fara caka mata akan ta da wuya da kuma hannu sannan ya koma kan wanta inda shima ya sassara shi.

Shafa’atu ta kuma ce ita ta nemi da a raba auren nasu inda kuma ta bukaci da abi mata hakkinta bisa raunukan da ya yi mata ita da dan uwan nata.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending