Connect with us

KANUN LABARAI

Kotu a Kano ta yankewa gawa daurin shekara guda a gidan yari

Published

on

Share

Rafi’atu Ilyasu

Kotun majistary mai lamba hudu da ke zamanta a gidan Murtala, ta yankewa wani mutum mai suna Abubakar Bello da tuni da aka ce ya mutu daurin shekara guda a gidan yari.

Kano Foucus ta ruwaito Mai shari’a Rakiya Lami Sani ce ta yanke hukunci ranar Laraba a nan Kano.

Tun da fari dai an gurfanar da Abubakar Bello a gaban kotun bisa laifin satar mota.

Sai dai ana tsaka da shari’ar ne aka gabatarwa da kotu takardu cewar wanda ake tuhuma ya mutu.

Wannan ce ta sanya mai shari’a ta rufe shari’ar tun da dai ba a shari’a ada gawa.

To sai dai bayan rufe shari’ar ne kuma aka hango wanda akace ya mutun yana yawo a gari abinsa.

Hakan ce ta sanya aka yi masa tarko da wata budurwa, aka kuma sake kamashi.

Hisbah ta bukaci masu laifi suyi sallah raka’a 50 kafin a kaisu kotu

Kotu ta daure matashi a Kano kan furucin kashe mahaifinsa

Kotu ta yankewa matasa biyu hukunci bulala 12 a Kano

Dan sandan kotu mai gabatar da kara ASP Ahmad Mukhtar ne ya sake gurfanar da shi gaban kotun bisa zarginsa da laifin satar mota da ake yi masa tun a baya.

Haka kuma mai shari’ar bayan nazari da bincike ta tabbatar da laifin da ake zarginsa da shi.

Mai shari’a Rakiya Lami Sani ta yankewa Abubakar Bello daurin shekara guda a gidan yari, ko kuma zabin tarar N50,000.

Sai dai kotu ta ce dole ne ya biya N750,000 kudin motar da ya sata tun a baya.

Barrister Tijjani Ibrahim shi ne lauyan gwamnati, ya shaidawa manema labarai cewa a baya an gurfanar da wanda ake zargi gaban kotu, sannan aka bashi dama ya kawo shaidu domin kare kansa amma sai ya bace bat.

Ya ce ana tsaka da haka ne wadanda suka karbi belinsa suka zo da takardun asibiti cewa Allah ya yi masa rasuwa.

Hakan ta sanya kotun ta rufe shari’ar, sai kuma yanzu aka sake ganinsa a gari.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending