Connect with us

KANUN LABARAI

Zanga-zanga: yadda aka kashe yarana hudu a Kano.

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Hajiya Hadiza Shareef da ke unguwar rijiyar lemo a nan Kano  ta ce yaranta hudu da ke yi mata aikatau aka kashe ya yin zanga-zangar @EndSARS a Kano.

A wata hira ta musamman da jaridar Kano Focus a ranar juma’a ta ce yaran nata na kular mata da gidan ‘Wanka da Bahaya’ da ke Middle Road a unuwar Sabon Gari.

Ta bayyana matasan da aka kashe da Abdurrahman Sobo wanda ya fito daga garin Minjibir kuma yake aikatau a hannunta tsahon shekaru biyu.

Sai Kuma Jamilu Muhammad da ke unguwar Zoo rood a nan birinin Kano da shi ma ya shafe sama da shekara yana yi mata aikatau,

Sai kuma na uku Aliyu Shehu da ake yiwa lakabi da Gatari mutumin sheka makaranta a nan birnin Kano.

Cikon na hudun shi ne Badamasi Ibrahim da ya zo ci rani daga Katsina, yake kuma zaune a unguwar Jaba.

Hajiya Hadiza ta ce mutum uku daga cikin wadannan an samu gawar su biyu ma har an yi musu jana’iza ya yin da daya har yanzu yake mutuware a asibitin Murtala.

Sai dai ta ce cikon na hudu wato Abdurraman Sobo an koneshi kurmus ne ba su iya tantance gawar sa ba kamar na ragowar.

Yadda al’marin ya faru

A cewar Hajiya Hadiza an mamayi yaran nata ne cikin dare  a ranar Talata da ta gabata inda wasu matasa dauke da makamai da galibinsu inyamuraine suka kewaye gidan da yaran nata ke yi mata aikatau da nifin Hallaka su.

“A ranar Talatar da ta gabata ‘Da’ na Arabi ya kirani a waya ya ce naje na debo yarana wato kannensa daga makaranta ana tashin hankali.

“Ba shiri na tafi na debo su, da yake suna karatu ne a makarantar Tony Chetta.

“Sai na ce mishi suma su rufe wurin nasu da suke sana’ar su taho gida, sai ya ce ba komai an kwantar da tarzomar.

Da magariba na sake kiransu na ce ku fito daga wurin nan kungani ya zama kamar fadan kabilanci da Inyamuran kunce suna ta dukan Hausawa, sai ya ce min ba komai, wuta ta lafa.” A cewar ta.

Cikin dare aka kai musu hari

Hajiya Hadiza ta kara da cewa bayan wannan tattaunawa da yaron nata ne kuma ta kara samun waya marar dadi cikin dare.

“Karfe 3:00 na dare sai Arabi ya sake kirana ya ce gabadaya Inyamuran nan sun sake yi musu kawanya.

“da yake yaran namu a ciki suke kwana kuma wannan gidan shi kadai na Hausawa a yankin, don haka suka mayar da hankali a kansa.

“Bayan da aka yi hatsaniyar da rana kura ta lafa shi ne fa suka sake komawa cikin dare suka yi musu kawanya suka kashe na kashewa suka kona na Konawa”. A cewar ta.

Da kyar muka sha da ranmu

Arabi Sahrif Hadi da ke zaman Da ga hajiya Hadiza da kuma ke kula da gidan wankan ya shaidawa Kano Focus yadda suka tsira da ransu kuma sauran abokan sana’ar sa suka salwanta.

Ya ce bayan kura ta lafa a zanga-zngar ranar Talata bayan magriba sai wasu gungun matasa da makamai suka taso musu kamar za su hallakasu.

“Sun yo kan mu da makamai muka ce musu mu ina ruwan mu ba fada muke da sub a, muka dai samu muka gudu muka shiga muka kulle.

“Sunyi ta kokarin balla gidan amma Allah bai basu sa a ba sai suka hakura suka koma.

“munan zaune cikin razani da firgici domin kowa ya kasa tafiya gida a nan muka kwana, da misalin karfe uku saura muka fara jiyo ihu da hayaniya sai wuta ke tashi ta ko ina.

“”suka zo suna dukan gidan suna mu bude idan ba haka ba za su hauro sai sun kashe kowa, suka bankara Kofar cikin ikon Allah basu samu sun karya ba.

“to bayan munji kamar sunja bayan ne wasu daga cikin mu sai suka fita suka ruga don menan ceton ransu ni kuma na tsallaka wani Hotel da ke kusa da mua na fake.

“shi Badamsi ya na fita suka bigeshi sai gawar sa muka gani da safe a cikin kwata, shi kuma Abdurrahman Sobo ga shinan kusa da Badamasi an saka masata taya an kone shi kurmus ko da dai bamu ganeshi ba amma dai ina kyautata zaton shi ne.

“Sauran yara kuma akwai sabbin gine-gine da aka yi da ba a kammala ba sai suka bude sokaway din suka shiga suka buya, wasu kuma suka buya cikin ciyayi, wannan shi ne abin da ya faru cikin dare.”

Arabi ya shaidawa Kano Focus cewar duk da wannan al’amari da ya faru cikin dare washe gari suka sake dawowa suka nemi balla gidan domin su cimmusu.

“bayan sun dawo washe gari ne suka kuma koramu muka shiga muka kulle yara suka ruga aguje neman mafita.

“Muna gani akan idon mu aka dauki Jamilu aka dannashi a cikin duron da suka kunnawa wuta ya kuma kone kurmus akan idon mu.

“Akwai wani Abuakar shima muna gani suka dannashi a cikin doron ya kone kurmus. A cewar sa.

Ya kuma ce kafatanin wadanda suka mutu an aike da gawarwakin su dakin adana gawarwaki na asibitin Murtala da ke nan Kano.

Haka zalika tuni wasu da ga cikin su ‘yan uwansu suka fara karbar gawawwakin su domin yi musu suttura.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending