KANUN LABARAI
Budurwa ta kashe kanta a Kano ta hanyar rataya

KANUN LABARAI
NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Aminu Abdullahi
Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.
Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .
Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.
Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.
Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.
Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.
Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.
Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

KANUN LABARAI
Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Aminu Abdullahi
Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.
Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.
Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.
“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.
“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.
Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.
Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.
Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

KANUN LABARAI
A harbe duk wanda aka gani da bindiga kirar AK47-Muhammadu Buhari

Mukhtar Yahya Usman
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin harbe duk wanda aka gani da wasu muggan makamai musamman ma bindiga kirar AK47 mutukar ba jami’in tsaro ba ne.
Kano Focus ta ruwaito cewar jami’in yada labaran shugaban kasar Malam Garba Sehu ne ya bayyana hakan ya yin da ya ke ztawa da sahsin hausa na BBC ranar Laraba.
Garaba Shehu ya ce shugaban kasar ya kuma bada umarnin a ragargaza dukkanin ‘yan ta’addan da suka ki su mika wuya.
Umarnin na shugaban kasa na zuwa ne jima kadan bayan da gwamnoni shida na yankin Arewa suka gudanar da wani taron yadda za su magance matsalar tsaro a jihohinsu.
Haka kuma gwamnonin sun bukaci fito da sabbin dabarun yaki da ga sojojin kasar nan domin dawo da zaman lafiya a yankunann da riki ya di-daita.

-
KANUN LABARAI4 months ago
Gwamnatin Kano za ta mayar da ma’aikatan wasu hukumomin ta zuwa makarantu
-
KANUN LABARAI4 months ago
Yadda muka samu silin gashin manzan Allah a Kano-Sheik Karibullah
-
KANUN LABARAI4 months ago
Angwaye a Kano na daga aure saboda hauhawar farashin siminiti
-
KANUN LABARAI4 months ago
Zanga-zanga: yadda aka kashe yarana hudu a Kano.
-
KANUN LABARAI4 months ago
Jin waka na kara imani- Ibrahim Khalil
-
KANUN LABARAI5 months ago
Zanga-zanga: Ana zargin mutane hudu sun mutu a Kano
-
KANUN LABARAI4 months ago
Dalilai biyar da ya sa mata suka fi son namiji mai gemu
-
KANUN LABARAI4 months ago
Yanzu-yanzu: Kungiyar musu shirya-fina-finan Hausa a Kano ta kori Rahama Sadau