Connect with us

KANUN LABARAI

Rashin filayen wasanni na kara sanya yara da matasa zama dakikai a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Wani masanin halayyar dan adam dake jami’ar Bayero a nan Kano  Aminu  Sabo Dambazau ya ce rashin filayen wasanni ga matasa na kara musu kuncin rayuwa da hakan ke haddasa musu  rauni fahinta a karatunsu.

Malam Dambaza ya bayyana hakan ne yayin zantawarsa da jiaridar Kano Focus a ranar Larabar da ta gabata.

Danbzau ya ce wata illar ta rashin samun damar yin wasanni na sanya matasa aikata mugayen dabi’u a cikin al’umma.

Ya kara da cewa wasanni na karawa dan adam karsashi da walwala da hakan ke dabe musa damuwa.

Dambazau ya yi kira ga gwamnati da ta daina gine filayen wasanni da ake dasu a cikin unguwanni duba da irin muhimmancin da suke dashi.

A nasa bangaren wani malami a sashen motsa jiki na kwalejin ilimi ta tarayya dake Kano F.C.E dakta Isyaku Labaran Fagge yace motsa jiki kantemaka wajen bungakasa lafiyar kwakwal.

Yace abin takaici ne yadda gwamnatoci ke gine filayen wasanni dake cikin unguwanni wanda kuma hakan ke baraza ga cigaban bangaren.

Ya ce yawan aikata laifuka da karuwar matsalar shaye shaye da ake samu a jihar Kano nada alaka da matsalar karancin filayen wasanni a unguwanni.

Fagge ya kuma shawarci gwamnati data bunkasa ragowar filayen da ake dasu ta hanyar gyarawa tare da samar da yanayin da ya dace don ciyar da harkokin kwallon kafa gaba a fadin jihar Kano.

Saidai kuma a wani bincike da jaridar Kano Focus ta gudanar ta gano yadda matasa a wasu unguwannin kan maida gefen titinan unguwannin su guraren buga kwallon kafa .

Yayin da wasu kuma kan zabi yin wasan kwallon kafar a tsakiyar layunka unguwannin su.

Wasu kuma matasan kan bar ma unguwannin nasu zuwa wasu unguwannin don samun gurin da za su yi wasanni musamman ma na kwallon kafa.

 

Najibu Ibrahim mai shekaru ashirin da biyu mazaunin unguwar Tukuntawa yace a shekarun baya basa shan wahala duk lokacin da zasu buga kwallon kafa.

Saidai yace sakamakon gine filayen wasannin unguwar da akayi hakan ta sa dole sai sunyi tafiya mai nisa kafin su samu filin da za su yi wasan kwallon kafa.

Shima wani matashi mai suna Tukur Muhammad yace sakamakon rashin filin wasa a unguwar su hakan tasa yasakale takalman sa.

Yace dole ce tashi ya dena buga kwallo saboda sai ya yi tafiya mai nisa kafin samun filin da zai buga kwallon kafa.

“Daga Gauron Dutse zuwa Kofar Na’isa sai na kashe kudi sosai sabo da nisa hakan tasa gaskiya bazan iya zuwa ba.

“Yakamata gwamnati ta rinka samar da filayen wasanni a unguwanni ta kuma daina gine wadanda ake dasu gaba daya,” inji shi.

Mubarak Muhammad wanda akafi sani  da Messi mai shekaru 26 yace kafin gine filin wasan unguwar su dake Sheka yana samu ya motsa jikin sa a kowace rana.

Ya kara da cewa ada koda ba zai buga kwallo ba to yakanje filin kwallo dake kusa dasu don samun nishadi.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending