Connect with us

KANUN LABARAI

Auren Janine da Sulaiman ya bar baya da kura a Kano

Published

on

Janine Sanchez Weds Sulaiman Isa Isa
Share

Zulaiha Dajuma

Tun bayan da aka daura auren Sulaiman Isa da Janine Sanchez a ranar Lahadin da ta gabata, al’umma a Kano ke ta tofa albarkacin bakinsu.

A zantawar jaridar Kano Focus da wasu matasa a nan Kano sun ce burin da mata ke da shi ne ya sanya ake haurowa har gida ana dauke musu mazajensu.

Ya yin da  wasu kuma sukace  kwadayin mazanne da neman biyan wata bukata ya sanya suke makalewa matan turawan, ya yin da wasu kuma saka ce hadi ne kawai daga Allah.

A soke lefe ko mu daina auren na gida

Wani matashi Abubakar Adamu Damisa ya ce yanzu lokaci ya yi da yakamata mata su cire buri da kwadayi su fuskanci abinda ya ke dai-dai.

“Ni a matsayina na saurayi zan iya cewa abune da muke farin ciki da shi, kuma Allah ya kawo irin su, suyi ta dauke samarin tunda su matanmu na nan burikan su sun fiye yawa”

“Turawa ba ruwansu da lefe da sauran abubuan da suka rufewa mata ido.

“Yanzu sai dai kawai a zo a dau ango ba kamar yadda aka saba gani ana daukan amarya ba.

“Idan matanmu basu dawo sunyi karatun ta nustuba, to tabbas za a fara ci gaba da duko turawa ana kyalesu gaba daya.

To sai dai a cewar wani matashi kuma dan gwagarmaya Aliyu Samb,  auren Sulaiman wani al’amari ne da ya zo da sabon salo.

Ya ce  auren ya nuna yadda zumunci ya ke da kuma damar auratayya a tsakanin muslmi da kuma ahlil kitabi.

“Ita baturiya, shi kuma dan Najeriya, akwai banbanci mutuka a tsakanin su ya zamanto kamar kulla zumunci ne.

“Irin wanna ake fata duniya ta samu, domin zai taimaka wajen wanzar da zaman lafiya a tsakanin kabilu mabanbanta da kuma addinai.

Ba zamu watsar da matan gida ba

Aliyu Samba ya kuma yi watsi da kalaman da ke cewa, mazan Kano za su watsar da matan gida domin su koma auren turawa.

Ya ce ai ba namijin da yake tsallake matar da Allah ya rubuta masa.

Idan baturiya aka rubuto masa to zai aura, idan kuma tamu ta gida aka rubuto masa to komai kwadayin sa da waccan din sai dai ya kalla daga nesa.

“Kaddarar mutune ke tabbata, ba auran matan turai ne zai sa matan mu na gida su kasa auruwa ba, haka auren mu na gida ba shi ne zai sa turawa su ki auruwa ba.

“Mazan turai za su iya zuwa nan su auri mata bakake, anyi, kuma anayi, mazan mu za su iya auran matansu matanmu za su iya auran mazajen su ba laifi bane” A cewar sa.

Kwadayi ne ya kaishi auren baturiya

Ita kuwa wata budurwa anan Kano Amina Adam ta ce, ita dai a fahintar ta kwadayi ne da son cimma wata manufa ya sanya Sulaiman Auren Janine.

Ta ce ta zauna a kasar turawa ta kuma ga yadda suke gudanar da rayuwar soyyayar su, a cewar ta ba ko sahakka lamarin su ba soyayya ba ce, illa nufin cimma wani buri.

“ Ban taba ganin wanan a matsayin soyayya ba, duk da dai jama’a na cewa soyayya ce.

“A matsayina na wadda ta taba zama a turai, duk da dai na san shi bai taba zama kasar turai ba, na ga irin wadannan  aururrukan.

Ana amfani da turawane domin a cimma wani burin na rayuwa, ciki kuwa har da neman takardar zama a turai.

Ta kuma ce dukkanin wanda ke ganin auren Sulaiman ya budewa maza Kofar auren turawa to shakka ba bu yana cikin hadari mai yawa, domin ba zai fahinci al’amarin ba har sai ya shiga cikn sa.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending