Connect with us

KANUN LABARAI

Korar Rahama Sadau ba zai tsarkake ‘yan fim ba-Jaruma Farida Jalal

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Jarumar fina-finan hausa Farida Jalal ta ta ce hukuncin da kungiyar masu shirya fina -finan Hausa ta MOPPAN ta yanke na korar Rahma Sadau sam bai dace ba.

Farida Jalal wacce ta kasance tsohuwar jaruma a Kannywood ta bayyana hakanne yayin tattaunawarta da jaridar Kano Focus a ranar Litinin.

Ta ce ba wannan ne karon farko da aka kori Rahama Sadau ba, a cewarta za su sake dawo da ita daga baya komai daren dadewa.

Ta kara da cewa kamata ya yi shugabanin kungiyar su samar da hanyoyi da za su dinga ladabtar da duk wani mutum da yake aikata laifi irin na Rahma amma ba kora ba.

Farida Jalal ta ce al’umma ba za su daina kallon  Rahma Sadau a matsayin jarumar masana’antar ba.

Kuma koda ta sake aikata wani laifin za a cigaba da alakanta ta ne da masana’antar.

“A da an kore ta kuma an dawo da ita, yanzun ma wannan kora ba za ta yi aiki ba, ” a cewar ta.

Jarumar ta kara da cewa kamata ya yi jaruman masana’antar su hade kansu tare da ciyar da masana’antar gaba, ba wai jifan juna da munanan kalamai ba.

“Abin takaici ne yadda wasu daga cikin mu suka dinga aibanta jarumar da yin tsinuwa gare ta bayan kuma kowannen mu mai laifi ne.

“Ta nuna nadamarta da ya kamata a ce mun yafe mata, muna yiwa Allah laifi kuma yana yafe mana matukar muka nemi gafarar” a cewar ta.

Jaruma Jalal ta ce komai ya faru Rahma Sadau ce ta jawowa kanta amma tunda ta tuba kamata ya yi a yafe mata.

Ta kuma yi kira ga jaruman masana’antar da su hade kansu tare da yin amfani da koyarwar addinin musulunci a duk kan al’amuran su na yau da kullum.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending