Connect with us

KANUN LABARAI

Dalilan da ke sa iyaye yiwa ‘ya’yansu auren dole

Published

on

Share

Wani masani kan zamantakewar dan adam a jami’ar Bayero dake nan Kano Malam Aminu Dambazau ya ce iyaye na yiwa ‘ya’yansu auren dole ne bisa dalilai da dama.

Malamin yayin zantawarsa da jaridar Kano Focus ya zayyana dalilai hudu a matsayin manyan dalilan da ke jawo auren dolen ga yara mata.

Ya ce dalilan sun hadar da kwadayi da talauci da kuma jahilci sai kuma al’ada.

Ya ce galibin  matan da shekarun su suka haura a shirin zuwa talatin sune suka fi fuskantar kalubalen auren dole.

Talauci

A cewar malamin iyaye suna yiwa ‘ya’yan su auren dole ne domin kubuta daga talauci.

Ya ce wasu iyayen kan zabi su aurar da ‘ya’yan su mata ga masu kudi domin dauke musu wahalhalun kudaden da za su kashe yayin aurar da ‘ya’yan nasu.

“Wani mahaifin yana tirsasawa ‘yar sa auren mai kudi koda kuwa bata son sa.

“Dalili kuwa shi ne wani zai dauki nauyi duk kudin da za a kashe a bikin.

“A karshe sai kaga yarinya tashiga wani hali wanda bai kamata ba,”

Jahilci

Ya kuma ce karancin ilimi da wasu iyayen ke dashi na taka rawar wajen kara ta’azzara dabi’ar auren dole.

Ya ce idan da ace iyaye sun san irin matsalar da hakan zai haifar bayan yin auren, ko kadan ba za su yiwa ‘ya’yan  su ba.

Malam Danbazau ya ce wasu iyayen na da karancin ilimin fahintar menene ma auren dole da hakan ke sa su aurar da yaransu ga wanda suke bukata ba tare da la’akari da matsalar da hakan zai haifar ba.

Kwadayi

Malam Aminu Dambazau ya ce galibin wasu iyayen na yiwa yaransu auren dole ne saboda kwadayin abin duniya kawai.

 

“Akwai iyayen da kwadayin abin duniya ke sa su yiwa ‘ya’yansu mata auren dole.

“Za kaga suna da rufin asiri amma idan wani yafito daga babban gida, ko yafi su arziki to a kokarin alakanta kansu da mutumin sai su aurar da ‘ya’yansu gareshi koda kuwa basa son sa.”

Dambazau ya ce neman suna da son a rakabu da jikin masu da shi na taka rawar gani wajen yin auren dole.

Malamin ya ce aurar da ‘ya mace ga wanda bata so, take hakkin dan adam ne da cin zarafinsa da ya zama wajibi a kawo karshen dabi’ar..

“Wasu ‘ya’yan kan kashe kansu koma su kashe wanda aka aura musu ta hanyoyi ma banbanta.

Al’ada

Haka zalika Dambazau yace wasu kabilun al’adarsu ce zabawa ‘ya’yan su miji ko matar da za su aura ba tare da sanin su ba.

A cewarsa Hausawa sun dade da dabi’ar  yiwa ‘ya’yansu auren dole, da a karshe hakan ke haifar da gaba a cikin iyali.

“Akwai matan dake sanadiyar mutuwar mazajensu ta hanyoyi daban daban sakamakon gina auren ba bisa ka’ida ba”

Ya kuma ce babu yadda za a yi ma’aurata su zauna lafiya matukar ba ayi auren bisa soyayya ba.

Ya ce wasu matan kan cigaba da mu’amala da samarin su nada duk kuwa da cewa akwai aure a kansu.

“A karshe sai kaga yarinya da aurenta amma tana karuwanci da wani namijin a waje,

“Hakan kuma ka iya sawa ta dauko wata cutar da za ta shafawa mijin ta na gida,”

Haka zalika ya ce koda an haifi ‘ya’ya basu cika samun kulawa yadda yakamata ba daga gurin mahaifiyarsu.

Ya kuma shawarci masu yin aure da su kauracewa auren wadanda suka nuna basa kaunarsu domin gujewa matsalar da kaje tazo.

Auren dole na tafiyar da farinciki na har abada

Wasu mata da jaridar Kano Focus ta zanta da su da suka tsinci kansu cikin auren dole, sun ce auren ya tafiyar musu da farinciki na har abada.

Hadiza Umar wata mata ce da aka yiwa auren dole ta ce duk da Allah ya albarkanceta da ‘ya’ya uku amma ta rasa farin cikinta tun daga lokacin da mahaifiyyarta ta aura mata wanda bata so.

Hadiza  mai shekaru Talatin  tace tana da wanda takeso da har sunyi alkawarin yin aure da zarar ta kammala karatun digiri.

Amma daga baya mahaifiyyar ta ta gabatar mata da wani mutum na daban a matsayin wanda zata aura.

Ta ce mahaifinta ya rasu wanda hakan yasa mahaifiyyarta itace kadai keda iko akan su.

“Saurayina na farko mai suna Aliyu Adam munyi matukar shakuwa kuma yana da rufin asiri daidai gwargwado.

“Ya kuma nemi ya turo magabatansa don ayi magana amma sai mahaifiyyata tace tana da wanda takeso ta aura min.

Ko menene mahangar addini

Wani malamin addinin musulunici a nan Kano da ke unguwar Sharada Muhammad Umar Sharada ya ce ba dai-dai bane iyaye su dinga yiwa yayansu auren dole.

Haka ya ce tilastawa yara mata fito da miji bayan basu da tsayayye ba dai-dai bane, kuma baya cikin koyarwar addini.

Malamin ya ce Allah da kansa ya ce kowanne  al’amari a kididdige ya ke kuma yana da lokacin faruwarsa.

A don haka ne ya ja hankalin iyaye da su dinga bin koyarwar addinin musulunci a koda yaushe.

A cewar sa akwai tarin matsaloli matukar akayi auren da ya saba koyarwar addinin musulunci.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending