KANUN LABARAI
Ko me yasa ‘yan KAROTA suka kauracewa titinan Kano

Mukhtar Yahya Usman
Wani abu da ba a saba gani ba a jihar Kano shi ne a wayi gari haka sidda ba tare da ganin jami’an KAROTA a kan hanyoyi ba.
Sai dai a zagayen da Kano Focus ta gudanar a yau ta gano yadda jami’an suka yi batan dabo a kusan dukkanin titinan jihar nan.
Wannan dai ta sanya jama’a da dama ke ganin hakan na da alaka da yajin aikin da yan Adai-daita sahu ke yi a fadin Birnin Kano.
Muhammad Ibrahim wani matashi ne da muka iske yana bada hannun a maimakon jami’an KAROTA a kan titin Gadon-kaya ya ce yadda yaga al’amura sun cakude ne yasashi tallafawa.
Ya ce yana tsammanin jami’an na KAROTA sun ki fitowa ne saboda tsoron kada masu zanga-zanga su farmusu.
“Kasan yau masu Adai-daita sahu suna yajin aiki, kuma fushi suke da hukumar KAROTA.
“Kaga ke nan idan suka fito komai zai iya faruwa domin kuwa za su huce a kansu.
Shi ma Nuhu Muhammad ya ce mataukar yan KAROTA suka fito bakin aiki a yau to ba shakka al’amarin ba zai yi kayau ba.
“Yan adai-daida sahu suna ciki da su, ka ga idan suka fito aiki ai kaddamar musu kawai za a yi.
“Sun yi dabara da suka ki fitowa, don ko ni nan ina ciki da su da sun fito sai a hankali kawai.
KAROTA ta kama inyamuri da ya yi safar tabar wiwi katan 60 zuwa Kano
KAROTA ta baiwa ‘yan kasuwar katako awanni 44 da su bar bakin titi
Za mu fadada ayyukan mu zuwa wasu hukumomin gwamnati-KAROTA
Shehu Muhammad wani matukin Adai-daida sahu ne ya ce tunda sun zalincesu ai ba za su iya fitowa su yi aiki ba.
“Ta yaya za su fito bayan sun zaluncemu, sun hanamu cin abinci, kasan ba za ta yiwu ba.
“Idonmu idonsu, sai an yi kare jini biri jini da su, kuma sai Allah ya saka mana.
“Wannan cin zaline ake yi mana, kuma ai gwamnatin za ta kare ne ba yadda za su iya, haka za su tafi su kyalemu.
Duk wani kokari da mukayi domin jin ta bakin hukumar ta KAROTA lamarin ya ci tura, domin kuwa mun kasa samun shugaban hukumar da kuma kakakinsa ta wayar tarho.

KANUN LABARAI
Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Mukhtar Yahya Usman
Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.
Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.
Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.
Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.
Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.
Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.
Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.
Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.
Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

KANUN LABARAI
NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Aminu Abdullahi
Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.
Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .
Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.
Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.
Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.
Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.
Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.
Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

KANUN LABARAI
Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Aminu Abdullahi
Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.
Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.
Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.
“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.
“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.
Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.
Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.
Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

-
KANUN LABARAI4 years ago
Budurwa ta kashe kanta a Kano ta hanyar rataya
-
KANUN LABARAI5 years ago
Gwamnatin Kano za ta mayar da ma’aikatan wasu hukumomin ta zuwa makarantu
-
KANUN LABARAI4 years ago
Yadda muka samu silin gashin manzan Allah a Kano-Sheik Karibullah
-
KANUN LABARAI5 years ago
Angwaye a Kano na daga aure saboda hauhawar farashin siminiti
-
KANUN LABARAI5 years ago
Zanga-zanga: yadda aka kashe yarana hudu a Kano.
-
KANUN LABARAI4 years ago
Jin waka na kara imani- Ibrahim Khalil
-
KANUN LABARAI5 years ago
Dalilai biyar da ya sa mata suka fi son namiji mai gemu
-
KANUN LABARAI5 years ago
Zanga-zanga: Ana zargin mutane hudu sun mutu a Kano