Connect with us

KANUN LABARAI

Da gan-gan gwamnati ta ki biyan kudin NECO-Iyayen yara

Published

on

Share
Aminu Abdullahi
Iyayen yara da dalibai na cigaba da kokawa bisa yadda gwamnatin jihar Kano ta gaza biyan kudin jarabawar kammala karatun sakandire (NECO) da dalibai suka rubuta a watannin baya.
Kano Focus ta ruwaito cewa tun a watan Janairun shekarar da muke ciki ne a ka saki jarabawar  ta (NECO)  ta makarantu masu zaman kansu, sai dai sakamakon daliban makarantu gwamnati ya gaza fita a jihar nan.
Wani mahaifi mai suna Abubakar Isma’il da yaron sa ya rubuta jarabawar a makarantar sakandire dake Sabuwar Kofar ya ce dansa ya samu gurbin karatu a jami’a da kuma ake gab da fara tantance su sai dai rashin sakamakon jarabawar l na neman yiwa yaron nasa kafar ungulu wajen samun gurbin karatu.
Ya ce tuni aka saki sakamakon jarabawar na makarantu masu zaman kansu, amma har yanzu gwamnati ta gaza biyan kudaden daliban da suka zana jarabawar a makarantun gwamnati.
Ya kara da cewa idan har gwamnati ta gaza biyan kudin don sakarwa ‘ya’yan su sakamakon jarabawar to la shakka  za su rasa guraben karatu a jami’a a wannan shekarar.
Balarabe Musa mahaifine da yaron sa ya rubuta NECO a Kwalejin Rumfa ya ce rashin baiwa ilimi muhimmanci ne yasa har yanzu gwamnati ta gaza biyan kudin jarabawar.
Ya kara da cewa ya kamata gwamnati ta duba halin da ‘ya’yansu ke ciki musamman yadda suke neman rasa guraben karatu.
Sadiya Hassan ta ce dama can gwamnatin jihar Kano ta saba yin jinkiri wajen biyan kudin jarabawar dalibai a jihar Kano.
Ta ce bai kamata a ce ana samun tasgaro a irin wannan al’amari ba duba da cewa hakan na kara haddasa lalacewar ilimi.
” Yarinyata ta samu gurbin karatu amma kaga idan ba taje da takardun shaidar kammala sakandireba ba za a tantance ta ba.
” Sai ta kara jiran wata shekarar tukunna a irin wannan ne kuma sai kaga karatun yara ya lalace,” a cewar ta.
Binta Garba da ‘yar ta ke karatu a makarantar sakandire ta Liman Idris Maikalwa a unguwar Na’ibawa ta ce tana rokon gwamnatin jihar Kano da tayiwa Allah da Annabi ta biya kudin jarabawar ‘ya’yan su.
“Saidai fa muka biya gwamnati kudin rubuta jarabawar nan naira dubu 12 da 500 kowa hakama nima na biyawa yarinya ta.
“Mun riga mun biya kudin mu amma meyasa gwamnati zataki biyan hukumar kudin don Allah a taimaka a biya don su samu su shiga Jami’a,” a cewar ta.
Sani Salisu Dan hassan shine shugaban kungiyar iyayen yara ya ce za su je duk inda ya dace don tabbatar da cewa an saki sakamakon jarabawar daliban.
Ya kara da cewa wannan rikon sakainar kashi ne da ake yiwa ilimi, duk da cewa kwamishinan ilimi yayi alkawari  za a saki sakamakon amma har  yanzu shiru.
Sai dai duk kokarin da muka yi don jin tabakin kwamishinan ilimi na jihar Kano Sanusi Sa’idu Kiru abin ya ci tura.
Sa’idu Kiru ya ce da wakilin namu da ya sameshi a ofis domin jin bayani.
Koda yaje sai kwamishinan ya ce yaje ya ga babbar sakatariyar ma’aikatar, inda itama tace masa ai sunyi waya da kwamishina ya koma ofishin sa.
Saidai duk da tsahon lokacin da ya dauka yana jiran sa amma bai samu damar ganin sa ba.
Wannan na nuna cewa gwamnatin Kano na son yin wasa da hankulan jama’a ne kawai amma Basu da abin fada

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending