Connect with us

KANUN LABARAI

Direbobin manyan motoci a Kano sun zargi jami’an tsaro da karbar cin hanci da rashawa

Published

on

Share

Direbobin mota a tashar Kano Line sun zargi jami’an KAROTA da ‘yan sanda da kuma hukumar Road Safety da tilastamusu bada cin hanci da rashawa.

Kano Focus ta ruwaito direbobin na cewa jami’an tsaron na karbar musu kudi naira dubu dai-dai a duk lokacin da za su shigo jihar Kano da safe.

Wani mai suna Abubakar Yusuf ya ce a duk lokacin da suka ki bayar da na goron, jami’an na kaisu ofis tare da rubuta musu wani laifin na daban da sunan cewa ya karya doka.

“Idan muka zo U-turn wanda daga shi sai Kano Line za ka shiga ka sauke fasinjanka wani lokacin akwai MTD suna yawan uzura mana.

“A kwai KAROTA akwai Road Safety, wani zubin kamen na ba gaira ba daliline za a zo a ce an kama ka, suna iya karbar dubu daya dubu daya da dari biyar,” a cewar sa.

Shima Husaini Adamu ya ce ya kamata akai musu dauki la’akari da cewar basu da wurin da yawuce nan domin gudanar da sana’o’insu.

“Baki suna shigowa amma sakamakon irinhaka yanzu duk sun hakura sun daina shigowa,” a cewar sa.

To sai dai kan wannan zarigine muka tuntubi hukumomin da ake zargi da karbar na goron a hannun direbobin inda kuma sukayi bayani.

Mai Magana da yawun hukumar Road Safety a  jihar Kano Kabiru Ibrahim Daura ya ce matukar direba ya karya doka dole za a kamashi.

Sai dai ya ce kamata ya yi masu korafin su je kai tsaye ofishin hukumar, su kai korafinsu matukar ana kamasu ba da hakkinsu ba.

“Amma idan laifi sukeyi aka kamasu kaga wannan ba abin yin korafi bane, sai dai mu basu shawara su daina aikata laifin.

Haka zalika itama hukumar KAROTA cewa ta yi masu korafin suna ajiye motocinsu ne a kan hanya bayan kuma haramunne yin hakan.

Mai magana da yawun hukumar Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa  ya ce babu wani jami’insu da zai ce a bashi kudi a hannu ya saki wani mai laifi ba tare da anje office ba.

A nata bangaren rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta ce batada masaniya kan zargin.

Abdullahi Haruna Kiyawa mai magana da yawun rundunar ya ce kamata ya yi direbobin su kai korafinsu ga shugabanin kungiyoyinsu ko rundunar ‘yan sanda kai tsaye.

Sai dai ya ce tun da sun samu korafin to za su bincika gaskiyar lamarin tare da daukar matakin da ya dace

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending