Connect with us

KANUN LABARAI

Ba za a bude bodar Najeriya ba-Nanono

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Ministan Aikin Gona na Kasa Muhammad Sabo Nanono ya ce babu ranar da za a buɗe iyakokin kasar nan.

Kano Focus ta ruwaito Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin taron bikin rabon kayan aikin gona ga manoman da ambaliyar ruwa ta rutsa da su a jihar Kebbi.

Nanono ya ƙara da cewa har yanzu gwamnatin tarayya ba ta shirya buɗe iyakokin ƙasar nan ba, domin har yanzu tana nan akan bakarta na ganin harkar noma a ƙasar nan ta bunƙasa.

“Manoma a ƙasar nan sun yi matuƙar ƙoƙari wajen noma kayayyakin abinci da su ka haɗa da Shinkafa da Gero da Dawa da kuma Riɗi. “Har yanzu gwamnatin tarayya ba ta shirya buɗe iyakokin ƙasar nan ba, hakan ne ya sanya gwamnatin ta shirya domin baiwa manoman da su ka haɗu da ibtila’in ambaliyar ruwa tallafi domin haɓaka noman rani.

“Domin hakan zai sanya su samu abin da su ka yi asara a lokacin damuna” In ji Sabo Nanono.

Da gaske ne an ce za a bude boda?

A makon jiya ne dai Ministar Kuɗi ta ƙasa Zainab Shamsuna Ahmed, ta ce za a iya buɗe kan iyakokin ƙasar nan ba da jimawa ba.

Zainab Shamsuna Ahmed ta bayyana hakan ne a lokacin da ta ke zantawa da manema labarai na fadar gwamnatin tarayya.

Ta ce kwamitin fadar shugaban ƙasa da aka kafa kan lamarin ya kammala aikinsa kuma ya bayar da shawarar a buɗe.

Ta ƙara da cewa nan ba da ɗaɗewa ba kwamitin zai gabatar da rahotonsa ga shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, daga nan kuma za a gabatar da sanarwa a hukumance kan lamarin.

Yaushe Aka Rufe?

Tun dai a cikin watan Agustan shekarar 2019 ne gwamnatin tarayya ta rufe iyakokin ƙasar nan da zummar daƙile yawaitar fasa-kwauri da kuma bunƙasa tattalin arziki.

Matakin rufe iyakokin ya ja hankalin mutane da dama a kasar nan tare da jawo ce-ce-ku-ce, inda wasu ke goyon baya wasu kuma ba sa goyon baya.

A cikin watan Maris din shekarar da mu ke ciki fadar shugaban ƙasa ta ce ‘yan kasar nan sun ga irin amfanin da rufe iyakokin ya yi a fannin tattalin arzikinta.

Malam Garba Shehu, kakakin Shugaba Muhammadu Buhari, wanda shi ne ya bayyana hakan, ya jaddada cewa ba za a bude iyakokin kasar ba sai gwamnati ta samu tabbaci daga wurin makwabtanta cewa ba za a su rika yin abubuwan da suka saba wa doka ba a kan iyakokin.

Labarai24

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending