Connect with us

KANUN LABARAI

Hausa fim: Yaron da yazo Kano daga Adamawa don ganin Ado Gwanja

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Abdullahi Muhammad yaro ne dan shekara 13 da ya taso  daga garin Yolan jiyar Adamawa zuwa Kano don kawai ya yi tozali da Ado Gwanja.

Kano Focus ta ruwaito Hukumar Hisbace ta kamoshi a lokacin da yake watangaririyar neman Gwanja a Kano.

A zantawarsa da mu a rananr Juma’a, Abdullahi ya ce ya na bukatar ya hadu da gwanjane domin suyi musayar fasahar waka.

Ya ce Allah ya yi masa baiwa ta waka da yake ganin idan suka hadu da mawakin, to lallai hakansa zai cimma ruwa.

Ya ce ko da yake babu wata shakuwa ko kusanci tsakaninsa da Gwanja amma dai yana ganinsa a fim da hakan ta sa ya taso har zuwa Kano domin su hadu.

Motar shinkafa na biyo

Abdullahi ya ce bayan da ya sanyawa zuciyarsa zuwa Kano ne, sai ya nemi motar da ke kawo shin kafa ya haye.

Ya ce ya buya a cikin motar da ake kawo shinkafar ne ba tare da sanin masu motarba har zuwa Kano.

A cewarsa matukar masu motar suka gane yana ciki, to shakka babu za su hana shi zuwa lamarin da ya sanya ya buya sosai cikin buhunnan shinkafar.

Rashin iyaye

A cewar Abdullahi iyayen sa duk biyun sun mutu, da hakan ta sanya yake rike a hannun yayasa.

wanan ce ta sanya yake rasa kulawar da yakamata daga hannu  marikin nasa.

Ko da aka tambayeshi baya tsoron in ya koma gida ya gamu da fishin yayan nasa, sai ya ce fada ne kawai zai yi masa in ta kama ya dake shi daga nan kuma ta wuce.

Matakin Hukumar Hisbah

Tuni dai Hukumar Hisba da ta farautoshi ta kammala dukkanin wasu shirye-shirye na mayar da shi gida.

A cewar jami’in hulda da jama’a na hukumar Lawal Fagge, an cike dukkanin takardun da suka kamata kuma za a sanya shi a mota zuwa garin su.

Ya ce suna da abokanan hulda a jihar Adamawa da za su aike da shi ta hannun su domin neman danginsa, a kuma danka shi a hannun su.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending