Connect with us

KANUN LABARAI

Lafiya jari: Illoli 10 da kaciyar mata ke haifarwa

Published

on

Share

 

Zulaiha Danjuma

Wani kwarraren likitan mata da ke asibitin koyar na jami’ar Jos Dakta Kenneth Egwuda ya bayyana matsaloli goma da kaciyar mata ke haifarwa musamman ga ‘yan mata.

Yayin tattaunawa ta musamman da jaridar Kano Focus likitan ya ce kaciyar mata na jawo matsalar da ba safai ake iya maganceta ba.

A cewar sa matsalolin sun hadar da shigar cuta, karewar jini, wahala yayin haihuwa, da rashin haihuwar ma baki daya, sai kuma yoyon fitsari da kuma rauni yayin kaciyar.

Sauran sun hadar da Kaduwa, da daukewar sha’awa da kuma daukewar dararjar mace sai kuma mutuwa.

Shigar cuta

Dakta Egwuda ya ce yin kaciyar mata na gayyato cutuka iri-iri da kayayyakin da akayi amfani da su wajen kaciyar ke haifarwa.

Ya ce wasu cutukan da ake dauka sakamakon yin afani da karafan kaciyar sun hadar da cutar kanjamau (HIV), da cutar hanta da kuma ciwon sanyi.

“Dukkanin wadannan cutukan ba wadanda za a dauke su da wasa ba ne.

“Ba ko shakka mata na iya kamuwa da wadannan cutukan sakamakon yi musu kaciya.

Haka kuma matakur aka kamu da cutukan ba a dauki mataki da wuri ba shakka babu za a rasa rai.

Rasa jini

Likitan ya ce yiwa mata kaciya na jawo rasa jini a jiki da hakan ke jefasu cikin hadduran kamuwa da cutuka daban-daban .

“Rasa jini sakamakon yiwa mata kaciya shi ne mafarin bude Kofar kowacce cuta a tare da su.

“Babu yadda za a yi ka cirewa mace wani abu a matucinta ka ce jini ba zai fita, kuma fitar da ya ke yi yana saba ka’idar yadda ya kamata da hakan ke zama babban hadari a gare su”.

Wahala yayin haihuwa

Likitan ya ce matan da ake yiwa kaciya na fadawa cikin matsala ya yin haihuwa da ka iya sanyasu rasa abinda ke cikin su.

“Suna cikin hadari mai tsanani ya yin haihuwa musamman ma lokacin da suka zo turo jaririn su waje.

Hakan kuwa na faruwa ne sakamakon yadda aka yayyanka hanyar da jarin zai fito ya yi rauni harma ya zama tabo.”

Rashin haihuwa  

Dakta Ggwudu ya kara da cewa kaciyar mata na iya jawo rashin haihuwa ga mata sakamakon matsalolin da ake samu yayin saduwa.

Ya ce matan da aka yiwa kwaciya na samun matsala sosai wajen samun ciki da haihuwarsa.

“A wasu lokutan daukar ciki kan zame musu matsala saboda raunukan da aka riga aka yi musu yayin kaciyar.”

Yoyon fitsari 

Haka zalika likitan ya ce yoyon fitsari wata babbar matsalace da matan da aka yiwa kaciya ke fuskanta.

“Idan tsautsayi ya sa aka yanko mace da nisa har aka taba mahadar fitar fitsari to hakan na haifar da yoyon fitsari marar tsayawa.”

“A wasu lokutan musamman ma wanzamai na yankewa har su ta ba blader da hakan ke  haddasa ,matsala domin idan an yanke ba zai sake tofowa ballantan ya koma ya rufe.

Rauni  

Dakta Ggwuda ya ce tabon raunin da ka yiwa mata yayin kaciyar na ci gaba da girma a  gaban mace lokaci bayan lokaci da hakan ke tsuke musu gaba.

“Tudun tabban da ke samu na toshe Kofar gabansu sosai da har ta kai mazajensu ba za su iya biyan bukatun su da su ba.

A cewarsa hakan kan jefa matan cikin matsanancin hali da wasu lokutan man har sai an yi musu tiyata.

dauke sha’awa 

Likitan matan ya ce yiwa mata kaciya na rage sha’awar su ainun da hakan ke sanyawa suji basa bukatar saduwa da mazajensu baki daya.

Haka kuma ya ce a duk lokacin da mazajensu za su sadu da su suna fuskantar zafi mai tsanani da ke jefa su cikin damuwa.

Wannan kuma na taimakawa wajen daina shawa’awa baki daya.

Kaduwa

Likitan ya ce a mafiya yawan lokaci matan da aka yi wa kaciya na kaduwa ainun da hakan ke sanya su cikin damuwa a kowanne lokaci.

“Matan da aka yiwa kaciya na fadawa cikin damuwa tsahon rayuwarsu sakamakon yadda aka basu wahala lokacin yi musu.

“Kaduwar da suke yi lokacin da suke ganin yadda ake zurmuka musu karfe mai kaifi a gabansu, kuma suji ana yanka wani abu jikinsu na haifar da kaduwa mai yawa da galibinsu ke sanya su jijjiga

Rasa darajar ‘ya mace

liktan matan ya ci gaba da cewa kaciyar mata na sanya mata suji cewa sun koma ba ya, ba kamar sauran ma ta ba.

Ya ce matukar sauran mata ‘yan uwanta da suka san anyi mata kaciya to suna daukarta wata daban a cikinsu da hakan ke sayanta taji ta zama koma baya.

“Wannan na da alaka da yadda mace ke kallon kanta a matsayin wata marar daraja a cikin mata ko da kuwa tana da dararjar.

Mutuwa

Dakta Ggwuda ya ce mafi tsanani ga dukkan haduran da aka lissafa shi ne mutuwa.

Ya ce abu ne mai sauki mace ta rasa ranta sakamakon kamuwa da cutukan da ke tattare da yin kaciyar.

Mai ya kamata jama’a su sani

Dakta Ggwuda ya ce duk da cewa a yanzu matsalar ta ragu a birnin sai dai kauyuka, akwai bukatar a ci gaba da wayar da kan jama’a har a kawo karshen matsalar.

A cewarsa ko kadan kaciyar mata bata haifar musu da da mai ido ta kowacce fuska.

Haza zalika ya ce yiwa mata kaciya bashi da wata fa’ida ta bangaren lafiya face jefa lafiyar tasu cikin matsala.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending