Connect with us

KANUN LABARAI

Shin da gaske ne maza na kukan aure?

Published

on

Share

Zulaiha Danjuma

kukan aure wani lamarine da aka saba gani ga mata musamman ma lokacin da aka dauke su za a kai su dakin mazajen su.

Sai dai wani bincike da jaridar Kano Focus ta gudanar ya nuna cewa dayawa maza ma na shan kuka lokacin bikin su.

A zantawar jaridar Kano Focus da wasu matasa a nan Kano sun ce tabbasa maza kan yi kukan aure bisa dalin shakuwa da uwa, numa farinciki, jin dadin mallakar amaryar da sauran su.

Shakuwa da uwa

Wani matashi a nan Kano Umar Faruq Musa da ke sana’ar daukan hoto ya ce ya sha ganin angwaye na rusa kuka ranar daurin auren su ko kuma awurin biki.

Ya ce wasu da ya gani suna irin wannan kukan tsananin shakuwa ce da mahaifiyar su ya sanyasu gurshekar kuka.

“Mun zo tafiya da shi domin kai shi dakin sa, nan take mahaifiyarsa ta fara kuka shima sai ya barke da kukan”

“A lokacin ma akwai wadanda suka nuna cewar yana namiji amma yake sheka kuka dan zai bar gida?  Sai dai a fahintata shakuwa da uwa ba wasa bane.

“Suma masu fadar hakan watakia basu shakun bane kamar shi” a cewar sa.

Farin ciki  

Haka zalika wani magidanci da ke unguwar Gaida a nan Kano Nafi’u Usman ya ce angwaye da dama na yin kuka dalin farin ciki.

A cewarsa wani angon bai taba tsammanin jama’a za  su taru saboda shi ba, amma da ya waiga ya ga irin jama’ar da suka taro dominsa farinciki kan saka shi kuka.

“A fahintata abune da ya kamata, dai-dai ne ango ya sha kukan sa lokacin biki ba gazawa ba ne farin ciki ne.

Idan farin ciki ya cikawa mutum zuciya ba kowane zai iya dannewaba, tilas wani sai ya amayar an gani” a cewar sa.
Haka dai wani magidancin Injiniya Aliyu Ibrahim ya  ce ya rarrashi angwaye da dama  da suka sha kuka lokacin bikin su.

“Abokina da ya yi kuka a bikinsa ya yi ne sakamakon ganin  abokanan arziki da suka halarci   daurin auransa.

“Ya fara godewa jam’a ne kawai sai muka ga idanunsa na rawa, ba jimawa kawai sai muka ji ya barke da kuka” ya ce..

Wahalar samun mata

Wasu matasan sunce angwaye na yin kuka ne domin yi wa kai barka da samun matar.

A cewar su wasu mazan har ranar da za a daura musu aure suna shakkun ko matar mallakinsu ce ko kuma za su iya rasa ta.

A cewar Usman Sa’idu da kyar ya rarrashi abokinsa da ya fara kukan barka-barka.

“Abokina da kyar muka rarrasheshi, saboda yunkurin salwantar masa da amaryar da aka yi,

“Danginta suna ta son hadata da wani na dangi sai da kyar Allah ya kwato ya bashi.

“Ai kuwa ana kammala daurin aurenne ya samu wuri ya dinga rusa kuka abin sa saboda ya tabbatar ya kubuta.

Ko ya da ce aga ango na kuka?

Wasu ba’arin matasan sunce ko kadan bai da ce ba aga ango na kuka, la’akari da cewar mata aka sani da yin hakan.

A cewar Malam Sa’idu mazaunin unguwar Jakara a nan Kano  namiji da karfin zuciya aka sanshi ba wai kawai saboda an daura masa aure ya kama kuka ba.

“A fahinta ta matukar namji ya fara da kuka tun daga ranar bikin sa to matarsa ta samu lagonsa .

“Haka kuma wadanda basu san dalilin kukan sa ba za su yi masa kallon kuriciya ne kawai” a cewar sa.

Ra’ayin mata

Sai dai daga bangaren mata kuma sun ce babu wani aibu dan namji ya yi kuka a bikin sa.

Rukaiyya Tijjani da ke sana’ar kwalliyar mata ta ce ko kadan babu abun kunya dan namaji ya sha kukan sa.

Ta ce wasu ma kafin aurensu sun shan yin kuka a gaban ‘yan matan su ballantana maganar aure.

Ta ce taga maza da suka yi kuka gaban yan matan su har kashi uku domin neman sasantawa bayan da suka samu matsala.

Sai dai a ra’ayin Khadija Sani Maitama  tace, matukar taga namiji yana kuka ranar auren sa to za ta yi masa kallon dan soyayya ne kawai.

Ta ce dukakanin wanda ya aibunta namiji don ya yi kuka akan matar da yake so tabbas bai samu wadanda za su yi kuka a kansu ba ne.

Bai  kamata namiji ya yi kuka ba

Wasu daga cikin matan ra’ayin su ya banbanta inda suka ce bai kamata namiji ya ya yi kuka ba sabo da kawai ana bikin sa

A cewar matashiya  Rabi’a Namaradda  bashi da ma’ana, a ga namiji na kuka a bikinsa.

“Gaskiya kamar ya bada kaine,  wasu ma cewa za su yi angontama sai da yayi kuku a ranar”

“Na taba zuwa wata walima naga ango na kuka mutane suka fara bai dace ba, bai dace na miji yayi kuka ba”

“Kamar ya rage martabar sane na mazaje, kamar a cikin mazajen ya dawo na kasan ne kamar shi ba gwarzon namiji bane” a cewar ta.

Haka zalika Amira Sani da ke unguwar ciranci a nan Kano ta ce duk namijin da yayi kuka a bikin sa to ba shakka sakarai ne

“Gaskiya ina yiwa duk namijin da ya yi kuka a bikin sa kallon sakarai”

“kuka a wurin namiji saboda ana yi masa aure shashanci ne a ganina gaskiya”

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending