Uncategorized
Yadda karancin ruwa da kwari ke illata harkar Noma a Najeriya

KANUN LABARAI
Yanzu-Yanzu: Ganduje ya dakatar da Abduljabbar Kabara daga yin wa’azi

Mukhtar Yahya Usman
Gwamnatin Kano ta dakatar da Malam Abduljabbar Nasiru Kabara daga yin wa’azi, tare da bada umarnin rufe masallacinsa.
Kano Focus ta ruwaito kwamishinan yada labarai na jihar Kano Malam Muhammad Garba ne ya sanar da hakan a daren Laraba.
Kwamishinan ya ce an dauki matakin kulle masallacin ne saboda dalilan tsaro.
cikkaken labarin na tafe……

KANUN LABARAI
PDP a Kano ta ce ba za ta shiga zaben kananan hukumomi ba

Mukhtar Yahya Usman
Jam’iyyar PDP, a Kano ta ce ba za ta shiga a fafata da ita ba a zaben kanan hukumomin jihar nan da ke tafe.
Kano Focus ta ruwaito shugaban kwamitin riko na jam’iyyar, DanLadi Abdulhamid ne ya bayyana hakan ya yin taron manema labarai a ofishin jam’iyyar dake nan Kano.
Danladi Abdulmumin ya yi zargin cewa an fitar da kudaden da suka wuce kima wajen yin zaben sannan kuma suna tsoron haifar da rikici yayin zaben.
Ya ce babu yadda za yi su shiga zaben da tuni Gwamnan Kano Ganduje ya rubuta wadanda za su ci.
Ya kuma ce gwamnati ta ware kudi kimanin naira biliyan biyu da miliyan dari uku kan zaben da sun riga sun san su za su baiwa kansu.
tuni dai hukumar zabe ta jihar Kano ta sanar da watan Janairun badi a matsayin watan da za ta gudanar da zaben kanan hukumomi da na kasila a fadin jihar nan

GAME DA MU
Yan sanda a Kano sun sake kana dan sahun da ke sauke fasinja ya gudu da kayansu

Aminu Abdulahi
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sake cafke direban adai-data sahu da ya kware wajen guduwa da kayayyakin fasinjoji ya yin da yake tuki.
Kano Focus ta ruwaito cewa an sake cafke direban adai-daita sahun ne mai shekaru 39 bayan da ya sake yin batan dabo da kayan wasu mata na kimanin naira dubu dari hudu a bakin barikin Bokabo.
Direban adai-daita sahun mai suna Muhammad Ahmad Muhammad Kabuga ya ce wannanne karo na biyu da aka sake kama shi da aikata irin wannan laifi.
Ya ce kaddarace ta sa shi yake aikata irin wannan muguwar dabi’a kuma yana fatan Allah ya shirye shi.
A nasa bangaren mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce sati biyu da suka gabata suka kama wanda ake zargin tare da gurfanar dashi a gaban kotu.
Kiyawa mai mukamin mataimakin sufurtandan ‘yan sanda ya ce kotu ta yanke masa hukuncin shekara biyu ko kuma biyan tarar naira dubu arba’in wanda kuma ya biya tarar nan take.
Saidai bayan da ya fito ne kuma sai ya sake yin awon gaba da kayayyakin wasu mata su biyar.
Kiyawa ya kuma ce wanda ake zargin ya tabbatarwa da rundunar cewa ya aikata duk kan lefukan da ake tuhumar sa da shi.
Ya kara da cewa bayan da suka ci gaba da bincike ne kuma sai suka same shi da jabun kudi kimanin naira dubu hamsin.
Ya kuma tabbatar da cewa yana siyan rafa daya a gurin wasu mutane akan naira dubu goma sha biyar kana daga bisani kuma ya shiga dasu cikin kasuwa.

-
KANUN LABARAI2 years ago
Budurwa ta kashe kanta a Kano ta hanyar rataya
-
KANUN LABARAI2 years ago
Gwamnatin Kano za ta mayar da ma’aikatan wasu hukumomin ta zuwa makarantu
-
KANUN LABARAI2 years ago
Yadda muka samu silin gashin manzan Allah a Kano-Sheik Karibullah
-
KANUN LABARAI2 years ago
Angwaye a Kano na daga aure saboda hauhawar farashin siminiti
-
KANUN LABARAI2 years ago
Zanga-zanga: yadda aka kashe yarana hudu a Kano.
-
KANUN LABARAI2 years ago
Jin waka na kara imani- Ibrahim Khalil
-
KANUN LABARAI2 years ago
Dalilai biyar da ya sa mata suka fi son namiji mai gemu
-
KANUN LABARAI2 years ago
Zanga-zanga: Ana zargin mutane hudu sun mutu a Kano