Connect with us

KANUN LABARAI

Idan muka fara ramuwa a kan ‘yan kudu abin ba zai yi dadi ba-Bashir Tofa

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban kungiyar dattawan Arewa Alhaji Bashir Othman Tofa yayi Alawadai da kinsan da ake yiwa ‘yan arewacin kasar nan musamman Fulani a kuduncin kasar nan inda ya ce matukar aka fara ramuwa to za a sha wahala kafin a shawo kan al’amarin.

Kano Focus ta ruwaito cewa Tofa ya bayyana hakane cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai ranar Talata a nan Kano.

Ya ce ba abune da za a yarda dashi ba yadda ake kashewa tare da raunata al’ummar Arewacin kasar nan a yankin kudancin kasar.

Ya ce a bayyana yake cewa akwai mumunan shiri da wasu keyi da zai haifar da rikici da ka iya sanadiyyar ruguza kasar baki daya.

“Abubuwa sun fara daukar dimi matukar ‘yan Arewa suka fara daukar fansa akan al’ummar kudu dake zaune a nan tofa zai yi wuya a shawo kan al’amarin.

“Makiya na gida da na waje, wasu ma jami’an tsaro sun san su, suna kulla kullar yadda zamu ci zarafin junanmu, ta yadda ba zamu sake dawowa kamar yadda muke ba da zarar an fara zubda jini.

“Babu wani bangare a kasar nan da yake zaune lafiya.

“ ‘Yan ta’adda na cikin gida da makota dama na kasashen ketare nata kokarin yin duk mai yiwuwa don ganin sun ruguza mana kasa,” a cewar sa.

Haka zalika yayi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya dauki matsalar tsaro da ta addabi kasar nan da kuma yadda ake kashe mutane ba gaira ba dalili da muhimmanci tare da daukar mataki na gaggawa don magance su.

“Nasan fadar shugaban kasa ta damu kuma ana tattaunawa akan batun amma akwai bukatar daukar matakai na gaggawa.

Ya kara da cewa idan har wani dan kasar nan ba shi da ikon yin rayuwa da gudanar da kasuwancinsa har sai an muzguna masa ko yi masa barazanar kisa a wani bangare na kasar nan, to babu wani mahaluki da yakamata a bari shima ya zauna a ko ina.

“Idan kuwa har hakane to bamu da kasa kuma wannan shi ne abinda makiyanmu ke fata kuma bai kamata mu bar suba.

“Wadancan shugabanni wawayene suda ‘yan amshin shatansu wadanda ke karfafa musu gwiwa korar wasu ‘yan kasa daga jihohin su,

“Ya kamata su tuna cewa suna da ‘yan uwa dake zaune a wasu sassan arewacin kasar nan.

“Dole ne su daina, ko kuma doka ta dakatar da su ta hanyar da ya dace,” a cewar sa.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending