Connect with us

KANUN LABARAI

Yadda sanyi ke hana matasa sallar asubah a Kano

Published

on

Share

Zulaiha Danjuma

Shigowar yanayin sanyi a jihar Kano da ma wasu jihohin ya sanya matasa da dama kauracewa fita sallar asubahi.

A zantawar jaridar Kano Focus da wasu matasa a nan Kano, sunce  yanayin sanyi kan sanyasu kauracewa masallatai musamman ma idan babu abinda za su dafa ruwa domi yin alwala.

A yanzu dai lokacin sallar asubahi a Kano shi ne 5:30 zuwa 5:32 a wasu masallatan.

Sai dai da yawa daga cikin matasan sunce yin sallah a irin wannan lokaci indai ba ruwan zafi suka tanada ba, yana basu wahala sosai

Sadiq Ibrahim mazaunin unguwar tukuntawane,  yace kafin shigowar sanyi baya makara wajen sallar asubahi, a cewarsa yana tashi kafin ma ladan ya kira sallah.

“Gaskiya kafin shigowar sanyi ina ga bana makara sallar asuba, dan lokuta da dama kan ma a kira sallan asuba na tashi”

“Da akwai wata rana da aka yi wani mukumukun sanyi idan nayi lilliba ma sanyi nake ji.

“Ina jin kiran sallar na dan leka waje nace kai bazan iya fita ba.

“Da yake mutun gwauro ba matace da shi ba, balle ace a dafa maka ruwan zafi”

“Yanzu gaskiya na kan jira rana ta dan fito sai inyi sallata gabaki daya, abin da nake yi kenan” A cewarsa.

Itama wata budurwa da ke zaun a unguwar Hotoro, Aishatu Ibrahim ta ce sanyin da akeyi yana hanata tashi daga gadonta da Asubahi.

“Sanyin nan yana neman takurani wajen hanani salla a kan lokaci”

“Ina tashi karfe 5:30, amma yanzu bana ma iya tashi daga gado sai karfe 6:00. Kuma idan na tashi karfe shidan sai na tabbatar da cewa inada ruwan zafi nayin alwalla”

“Yawanci nakan tanadi ruwan zafi kafin na kwanta bacci, saboda ba zan iya yin anfani da ruwan sanyi wajen alwalaba.” A cewarta.

Shi ma wani dalibi a jami’ar bayero Nura Yusuf yace yanayin sanyi yana hana shi alwalar sallar asuba.

“A halin da muke ciki muna kokarin mu tanadi ruwan zafi dai-dai misali idan ba a samuba kuma, nakan yi anfani da ruwan rijiya”

“Yau dai nayi alwala a kan lokaci amma nayi anfani da ruwan rijiyane, da yake shi yana da dan dumi, ba zai takuramin ba.

“Gaskiya na dan yi fashin salla tunda aka fara sanyin nan amma bana wuce karfe 6:00” a cewarsa.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending