Connect with us

KANUN LABARAI

Mata a Kano na murna da kulle gidajen Kallo

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Mata da dama ne a nan Kano ke nuna farincikinsu tare da yabawa gwamnati kan matakin da ta dauka na kulle gidajen kallo a daukacin jihar nan.

Kano Focus ta ruwaito galibin matan na korafin yadda mazan ke shigar musu hakki matukar aka ce ana wasan kwallon kafa.

Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da jama’a ke ci gaba da kiraye-kirayen a bude gidajen Kallon.

A cewarsu kulle gidajen kallon ba abin da zai haifar sai jefa al’umma cikin kunci da damuwa.

Gidan kallon ball na raba soyayya

Hussaina Adam wata budurwace a nan Kano ta ce gidan kallon ball ya sha sanyata fada da samarinta, a cewarta indai aka ce akwai ball to ko ba yadda za a yi samarinsu su je zance wurinsu.

“Duk lokacin da zaizo gurina matukar ya yi dai-dai da lokacin da za a haska wani wasa a gidan kallo baya zuwa.

“Sai ya ce min zaije kallon wasan Manchester, ko Real Madrid, a karshe ma sai dai mu sake tsai da wata ranar.

A gaskiya gidajen kallo na bata min rai,” a cewar ta.

Sakina Abdulmalik wadda matar Aurece ta ce, mijinta baya zama a gida da daddare matukar za a yi wani wasa to zai tafi gidan kallo.

Ta kara da cewa da zarar yadawo daga kasuwa da yamma, a nayin salar magriba yake fita zuwa gidan kallo, kuma ba zai dawo ba sai kusan karfe goma sha biyun dare.

“Kaga duk sanyin nan da akeyi sai yaje, amma jiya da daddare ba inda ya fita saboda an rufe gidajen kallon, wannan hukunci ne mai kyau,” a cewar ta.

Nafisa Tijjani itama wata budurwace a nan Kano, ta ce ta rabu da samari da dama sakamakon zuwa gidan kallon kwallon kafa.

A cewarta lazimtar kallon da suke yi ya sanya bata samun kulawar daga gare su.

Ta kuma ce idan da ace gwamnati za ta rufe gidajen kallon har a bada ma da tayi farin ciki da haka.

“Mu mata masu aure da marasa aure bama jin dadin gidajen kallon nan wallahi,” a cewar Nafisa.

Maza za su damemu da zaman gida

Su kuwa wasu matan cewa sukayi bai kamata gwamnati ta rufe gidajen Kallo ba domin wata hanya ce da ke samarwa maza nishadi.

Khadija Abba Garba ta ce kokadan bata ji dadin rufe gidajen kallon ba domin yana samar da nishadi.

Ta ce yanzu da aka rufe gidajen kallon mazajen su za su dinga  damunsu da zaman a gida su kuma fara sa musu ido.

“Nikam bana goyan baya gaskiya, kaga wani lokacin ma mai gidana yana tafiya dani classic gurare da ake kallon kwallo.

Ko ina ra’ayin samari?

Sai dai a nan kuma magoya bayan kungiyoyin kwallon kafa a jihar Kano ne ke cigaba da kokawa kan yadda gwamnatin ta kulle gidajen kallon.

Hassan Ibrahim cewa ya yi baya goyan bayan rufe gidajen kallon duba da yadda harkokin wasanni ke daukewa matasa kewa tare da kara hadin kai a tsakanin su musamman idan suka je gidajen kallon kwallon kafa.

Ya kara da cewa idan har yazama dole a rufe gidajen kallon to yakamata gwamnatin ta raba musu da ta wacce za su rinka yin amfani da ita don kallon wasannin da akeyi ta shafukan internet.

“Ni kaga bamu da dammar da zamu iya kallon wasan kwallon kafa a gida don ba zamu iya siyan kati ba kuma ni masoyin kungiyar Manchester ne dole idan inaso na kalli wasan mu to sai nazo gidan kallo.

Aliyu Rabi’u Neymar ya ce bashi da gurin da a yanzu zai samu ya rinka kallon wasannin da ake haskawa na gida da na waje kasancewar an rufe guraren dake haska wasannin.

“Kaga dai bani da ilimin boka balle na kalla ta yanar gizo kamar yadda wasu ke cewa za su koma kalla ta internet to mu ya za ayi damu kenan.

“Idan nadawo daga gurin aiki idan dare yayi ba indai nake samun nishadi sama da gidan kallon, a cewar sa.

Muzammil Umar ya ce a yanzu zai koma kallon wasannin ne a gida tare da iyalansa saidai ya ce kallo a cikin mutane da yawa yafi dadi.

“Duk lokacin da na kalli wasa a gida bana samun nishadi kamar yadda zan fita waje. a kalla a cikin abokanai na muyiwa juna ruba,” a cewar sa.

Isma’il Kabuga  ya ce rufe gidan kallo zai kawo koma baya ga harkokin wasannin ga matasa kasancewar gidajen kallon na debe musu kewa idan suka dawo daga kasuwa ko gurin aiki.

“Rufewar ba alheri bane don yanzu wasu za su koma zaman majalissa ai ta musu wanda daga karshe ma ai ta samun rigima a tsakanin.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending