Connect with us

KANUN LABARAI

Tsadar man kuli ta sabba hauhawar farashin kosai da awara a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hauhawar farashin man gyada a Kano ya sabba karuwar farashin kosai da awara da sauran kayan da ake sarrafawa da man gyada.

Kano Focus ta ruwaito a ‘yan kwanakin nan kosai da awara da fanke suka yi tashi gwauron zabo sakamakon karuwar farashin man gyada a fadin jihar.

Binciken da Kano Focus ta gudanar ta gano cewar a baya dai ana sayar da kwalbar man kuli akan N450, da a yanzu kuma ake sayarda kowacce kwalba akan N650 zuwa N700.

Haka zalika a yanzu ana sayar da karamin galan  akan N5500, sabanin yadda ake sayar dashi a baya da bai gaza N300 ba.

Kosai N10 duk guda daya

Hajiya Aisha Sulaiman wata mai sana’ar tuyar kosaice a nan Kano, ta ce ya zama dole ta mayar da sakin kosai daga N5 zuwa N10 sakamakon tsadar da man gyada yayi.

A cewarta matukar bata kara farashin ba to ba za ta iya mayar da kudin da ta kashe ba ballantana ta ci riba.

“Ya zama dole nayi hakan, idan ba haka ba bazan maida kudina ba.

“Wake ya yi tsada, muna siyan kwano akan N800 ga kuma mai shima yadda kullum yake kara kudi.

“Mankuli ma ana saida shi ne akan N800, to kaga bamu da zabi tunda ba zamuyi tuya da manja ba.” a cewar ta.

Biyu 50 muke sayar da fanke 

Ita ma Rukayya Muhammad da ke zaune a unguwar Tukuntawa dake sana’ar tuyar fanke ta ce kafin karuwar farashin mangyada tana saida fankenta akan naira goma duk guda daya.

Sai dai ta ce a yanzu dole ya sanya take sayarwa aka N50 duk guda biyu.

Ta ce duk da ta kara kudin amma mutane na cigaba da zuwa siya sai dai ba kamar a bayaba, lokacin da take sayarwa akan N10

“Ni kaga jarka nake siya amma wallahi a hakanma dakyar nake maida kudi na, kaima dai kasan yadda abubuwa suke tsada kulllum abubuwan kara kudi suke yi.

“Wasu idan suka zo siya dana fada musu yadda na koma siyarwa sai suyi tafiyar su, basa dawowa, don ranar da na fara canza farashi ma saida nayi kwantai,” a cewar ta.

Munfi sayar da awara akan uku N50

Talatu Gambo dake sana’ar a wara akan titin Gidan Zoo ta ce duk da kudin wake ya karu amma tana siyar da a wararta duk guda daya akan naira goma.

Sai dai ta ce a yanzu da farashin mangyada ya karu ta koma siyarwa akan guda uku naira hamsin.

“Saboda a gefen titi nake ciniki, shiyasa koda na sauya farashi ana cigaba da siya,

“Haka kuma ko yanzu farashin ya ragu to nima zan rage nawa farashin ya koma kamar da.

“Ni dai dana tambaya meyasa kudin mangyadan ya karu sai aka cemin wai yanzu ba a noma gyada, a kasar nan yawanci ana kawo ta ne daga Senegal,” a cewar ta.

In makomar jama’a?

Jama’a da dama da Kano Focus ta zanta dasu kan wannan kari da aka samu, sun nuna rashin jin dadinsu da halin da aka tsinci kai a ciki.

Wani matashi Ibrahim Isma’il da muka iske a layin siyan kosai yace kwanaki uku da suka gabata N5 ya sayi kosan duk guda daya sai dai yanzu ya koma N10.

“Kwana uku da nazo na siyi kosai duk daya N5, amma a yau da na dawo ana saida guda daya N10.

Haka na hakura nasiya saboda iyalina ta damamin koko kuma ba zai shawu ba babu kosai.

“A da ina siyan na N200 amma yau sai da na siyi na N500 saboda farashi ya tashi.” inji Ibrahim Isma’il.

Abubakar Abdulaziz da muka tarar shima yaje siyan kosai cewa ya yi ba zai iya siyan kosai ba a halin yanzu , duba da yadda aka kara masa kudi.

Ya ce ada yana siyan na dari da hamsinne wanda ake bashi duk guda daya a N5 sabanin yanzu da aka ce masa N10.

Ko hakan ya shafi mata a gida?

Sadiya Hassan uwargidace da ke zaune a unguwar Tukuntawa ta ce a yanzu ba a samun man gyada na N50 sabanin yadda a baya ake basu

“A watannin baya N50 ko N100 ta isheni nayi miyar kuka ko miyar shinkafa, amma yanzu sai na saka N150 nake iya siyan man da zanyi girki dashi.

“Kuma kudin cefanen da ake bamu ba karuwa yayi ba, a haka muke riritawa mu girka koda babu dadi don girki ba zai yiwuba idan babu mai, shi kansa yanzu manjan tsada yake yi,” inji Sadiyya.

Jamila Muhammad cewa ta yi a yanzu suna yin girkine  kawai da hikimomi tunda dai abubuwa sun ta’azzara.

“Gaskiya ni kaga mai gidana baya son girki da manja, kuma yanzu mangyadan ya yi tsada, hakuri kawai ake y, ni a yanzu ma nafi jika garin kwaki musha da yarana, saboda tsadar da man yayi,” a cewar ta

Ko me dillalan man ke cewa?

Abdullahi Adamu dake sana’ar sayar da mangyada a kasauwar Rimi ya ce watanni biyu da suka gabata suna siyar da mangyada duro guda akan N170,000, amma a yanzu suna sayarwa ne aka N190,000.

Ya kuma ce suna sayarda yaluwar jarka akan N19,500, sai kuma karamin galan suna sayarwa akan N4000 sai kuma kwalba daya akan N650.

Ya kuma ce tashina man na da nasaba da gyadar da ake sarrafawa domin yin mangyadar, ana shigo da ita ne daga kasashen ketare.

A cewarsa hakan ya farune  sakamakon karancin noman gyada a jihar nan da ma kasa baki daya.

Saidai ya ce farashin yana hawa da sauka ne a galibin lokuta.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending