Connect with us

KANUN LABARAI

An kubutar da matar da aka yankawa wuya, aka kuma soketa a wuri 15 daga mutuwa a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wani matashi mai suna Al’amin Mohammed Bello mai shekaru 20 da wasu mutane uku bisa yunkurin hallaka wata mata a unugwar Guringawa dake karamar hukumar kumbtso, bayan da suka yankamata wuya suka kuma soketa a wuri 15.

Kano Focus ta ruwaito cewa mai magana da yawun rundunar Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana haka ga manema labarai a ranar Laraba.

Kiyawa ya ce a ranar 14 ga watan da ya gabatane wanda ake zargin ya shiga gidan matar mai suna Yusrah Zakari mai shekaru 20 tare da abokanansa  suka kuma yankamata wuya da sauran sassan jikinta sannan suka sace motarta suka gudu.

Acewarsa sun samun korafin ne daga mijin matar Abba Adam jami’an su je wurin, suka kuma dauketa zuwa asibitin Aminu Kano da a nanne aka ceci rayuwar ta.

Kiyawa ya ce rundunar ta samu nasarar cafke wanda ake zargin ne kwanaki talatin da biyu da faruwar alamarin tare da motar da suka sata.

Ya ce wanda ake zargin ya amsa laifinsa, Inda ya bayyana wadanda suka yi fashin tare da Abubakar Hassan mai shekaru 28 da Yusuf Lawan 21 ma zauna unguwar Sabuwar Gandu.

Sai Yahaya Salisu mai shekaru 28 dan unguwar Sheka duk a karamar hukumar Kumbotso.

Ya kuma ce zasu gurfanar da wadanda ake zargin da zarar sun kammala bincike.

‘Yan sanda sun kama guda cikin wadanda suka hallaka dattijo a Kano

Kotu ta yankewa matasa biyu hukunci bulala 12 a Kano

Rundunar ‘yan sandan Kano ta kubutar da attajirin Minjibir da aka yi garkuwa da shi

A nata bangaren Yusrah Zakari ta ce mijin ta ya fita lokacin da lamarin ya faru, a cewarta ta shiga kitchen don ta zuba abinci sai kawai gani tayi annufota da wuka daga nan ba ta sake sanin abinda ya faru ba.

“Bayan suka na a wuya sun soke nu a wuri shabiyar a jikina.

“Sai kawai ganina nayi a asibiti, naji dadi sosai da aka kamasu kuma ina fatan za a bi min hakki na,” a cewar ta.

Shima daya daga cikin wadanda aka kama mai suna Al’amin Mohammed Bello ya ce sun shiga gidan matarne a Sabuwar Gandu don satar mota.

“Mutum biyu suka tare kofa ni da Yusuf sai muka shiga ciki na dauki mukullin motar zamu fita sai ta janyo Yusuf shi kuma ya buga mata wuka a wuya.

“Shi ne muka dauketa muka sakata a cikin bandaki daga nan na dauki motar zuwa Kaduna ni kadai dan na sayar motar mu raba kudi,” a cewar sa.

Ya ce sunyi karatu a gidan mahaifinta kafin rasuwarsa sai dai bayan da ya mutu ne sai suka yi farin ciki da hakan tare da hada baki don aikata laifin da ake zargin su akai.

“Na batawa iyayena da ‘yan uwana, suna basu taba tsammanin zan aikata haka ba ina matukar nadama,” inji shi.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending