Connect with us

KANUN LABARAI

Muhimman abubuwan da suka faru a Kano cikin shekarar da muke bankwana da ita

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

A yayin da muke bankwana da shekarar 2020 Kano Focus ta yi nazari kan muhimman abubuwan da suka faru a jihar Kano da al’umma ba za su mace da shi ba.

Shekarar 2020 shekara ce da ta zo da sammatsi iri-iri da suka dagula lissafin al’umma da tabbas jama’a za su dade suna tuna ta.

Zuwan baturiya Kano

Janine Sanchez Weds Sulaiman Isa Isa

A cikin watan Janairun shekarar da muke bankwana da ita ne wata baturiya mai suna Janine Sanchez ta zo Kano domin auren wani matasi dan asalin unguwar Panshekara da ke nan Kano.

Zuwan baturiyar dai ya jawo ce-ce kuce a tsakanin al’umma, inda wasu ke ganin sa ce ta zo yi, yayinda wasu ke ganin wata bukata ce da ita akan sa ya sanya ta biyo shi.

Haka zalika wasu ba’arin al’umma na ganin cewa kwadayi ne irin na Sulaiman ya sanya shi soyayya da baturi.

To koma dai mene yanzu haka an dauran auren Sulaiman da baturiya kuma sun koma kasar Amurka.

Bude kotun daukaka kara a Kano

A rananr 11 ga watan Fabrairun shekarar da muke bankwana da ita ne aka bude kotun daukaka kara a Kano.

Shugabar kotun daukaka kara ta kasa Zainab Bulkacuwa ce ta jagoranci bude kotun domin saukaka al’amuran shari’a a kasa.

Haka zalika bayan da aka bude kotun an turo mai shari’a Abubakar Datti Yahya a matsayin alkalin kotun, yayin da mai shari’a Habib Adewale da kuma A.A Wambai za su dafa masa.

Idan za a iya tunawa kafin bude kotun, sai anje Kaduna ko wata jihar kafin a daukaka kara akan dukkan wata shari’a, amma da aka bude kotun an samu sauki kan wannan.

Tube Sarki Sunusi

A ranar 9 ga watan Maris din shekarar da muka yi bankwana da ita ne gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya tunbuke Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II.

Gwamnan ya ce ya dauki matakin tunbuke Sarkinne bayan da ya samu amincewar dukkanin ‘yan majalisar Zartaswarsa.

Haka zalika ya ce ya tunbuke sarkinne domin a kare mutunci da al’ada da kuma addini da ya yi zargin sarkin na watangaririya dasu.

Aminu Ado ya zama sarki

A dai wannan rana da aka cire Sunusi ne kuma aka sanar da Aminu Ado Bayero a matsayin sabon Sarkin Kano.

Anjiyo sakataren gwamnatin jiha Alhaji Usman Alhaji na cewa an zabi Aminu Ado a matsayin sabon Sarkinne domin cancantarsa da kwarewarsa akan sha’anin mulki.

Kafin nada shi Sarkin Kano shi ne Sarkin Bichi na farko a tarihi tun da aka kafa masarautar.

Idan za a iya tunawa Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya kirkiri sabbin masarauti hudu baya ga ta Kano inda ko wacce ya yi mata sabon sarki.

Bullar Korona a Kano

A rananr 11 ga watan Afrilun shekarar 2020 ne aka fara samun bullar cutar kwarona a Kano.

Rahotanni sun ce wanda aka fara samu din ya shigo jihar  Kano ne daga Birnin tarayya Abuja.

Haka kuma bayan an gwadashi ne aka killace shi a inda aka tanada domin killace masu dauke da ita a asibitin Kwanar Dawaki.

Kuma tun da ga wannan lokacine aka ci gaba da samun bullar cutar har zuwa wannan lokaci.

Buhari ya kulle Kano

A ranar 27 ga watan Afrilun shekarar da muka yi bankwana da ita ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya dokar kulle a jihar Kano ta sati biyu saboda bullar cutar Covid-a19 a Kasa.

Shugaban kasar ya ayyana dokarne lokacin da yake bayani ga al’ummar kasa kan halin da ake ciki dangane da cutar Covid-19.

Ya kuma bukaci al’umma da su zauna a gida ba shiga ba fita ba mu’amala da juna tsahon wadannan kwanaki.

Mace-macen Kano

A watan Afrilun shekarar bara ne dai aka dinga samu yawaitar mace-mace a Kano da aka kasa gane dalilinsu.

Sai dai wani likita a nan Kano Isa Abubakar ya ce mace-mace na afkuwa ne saboda dalilai guda uku.

Na daya zai iya kasancewa masu dauke da cutar Korona ne da ba a gwada an tabbatar da su ba.

Na biyu akwai mutane masu bukatar kulawar gaggawa ta likita amma saboda bullar Korona anyi watsi dasu.

Sai na uku ya ce marasa lafiya da yawa na kasa zuwa asibiti saboda kulle, suma kuma asibitocin basa karbarsu.

Soke bukukuwan salla

A ranar 18 ga Mayun shekarar bara ne gwamnatin Kano ta ce ta suke dukkanin shagulgulan Sallah sakamako bullar annobar Korona.

Ko da ya ke gwamnati ta bada kofa aje masallacin idi a yi salla amma da sharadai masu tarin yawa.

Karo biyu ke nan a wanna shekara ana hana bukukuwan salla, da ya hadar da  na sallah karama da kuma babbar sallah

Mutuwar Umar Sa’idu Tudun Wada

A ranar 30 ga wantan Yuni ne fitaccen dan jaridar nan na Kano Umar Sa’idu Tudun Wada ya rasu sakamakon hadarin mota.

A cewar makusacin sa Umar Sa’idu Tudun Wada ya yi hasashen mutuwasa  mako guda kafin ya rasu.

A cewarsa hakan ce ta sanya yayi ta aikata abubuwan alheri daf da rasuwar tasa domin neman kusanci ga Allah ta’ala.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending