Connect with us

KANUN LABARAI

IAR ta samar da irin masara da ke jure fari, kuma tsutsa ba ta ci

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Cibiyar nazari da bunkasa al’amuran noma ta jami’ar Ahmadu Bello wato Institute for Agricultural Research (IAR) ta ce nan da shekarar 2022 za ta fito da sabon irin masara da ke jure karancin ruwa kuma tsuta ba ta iya ci da ake kira TELA maize.

Kano Focus ta ruwaito shugaban cibiyar Farfesa Isyaku Muhammad ne ya bayyana haka ya yin taron jin ra’ayoyin manoma kan yadda za a rungumi sabuwar fasahar da ya gudana ranar Talata a Kano.

Farfesa Isyaku ya ce matukar manoma suka rungumi wannan sabuwar fasaha to shakka babu za su samu amfanin masara da ya zarta wanda suka saba samu idan sun yi noma.

Ya ce cibiyar ta dade tana nazari kan yadda za a samar da wannan iri da zai taka rawa wajen inganta noman masara, ya kuma taimakawa manoma rage kudaden da suke kashewa wajen nomanta.

Sabuwar fasahar mafita ce ga manoma.

Farfesa Isyaku ya ce sau dayawa akan zo da sabuwar fasaha, kuma yana da wahala al’umma su karbeta nan ta ke ba tare da jin dar ba.

Manoma ma ba a barsu a bayaba wajen kaucewa a abinda ba su sanshi ba.

A don hakanne ya bukaci manoman da kada zuciyarsu ta kadu, da zarar wannan iri ya fito, to su karba su gwada za kuma su ga nasarar da hakan zai haifar musu.

Ya ce idan manomi yana samu buhu ashiri a gonarsa da tsohon irin masara, idan aka samar da wannan na zamanin to manomi zai iya samu buhu 35 zuwa 40.

Sabuwar fasahar za ta magance yunwa a kasar nan

Haka zalika Farfesan ya ce idan manoma suka fara amfani da wannan iri, to ba shakka zai taimaka wajen samar da abinci mai yawa da zai yi maganin yunwa a kasar nan.

Ya ce hatta hanyoyin samar da kudin shiga a kasar nan za su habaka ta dalilin wannan sabuwar fasaha.

A cewarsa ana gudanar da sana’o’I da dama da suka hadar da abincin kaji da sauran abubuwa da masara.

Inda ya ce matukar za a bunkasa wadannan sana’o’I jama’ da dama za su samu aikinyi za kuma a fita daga kangin yunwa.

Ko me manona ke cewa?

Ko da ya ke wasu daga cikin manona da aka zanta da su ya yin taron jin ra’ayin sun nuna jin dadin su dangane da sabuwar fasahar amma suna bukatar akara fahitar da su muhimmancin wanna iri.

A cewar Yusuf Ibrahim zai yi amfani da wannan fasaha da zarar an fito da ita domin ya tantance tsaba da tsakuwa.

Ya ce ko shakka babu ya yarda da binciken kimiyya, kuma zai karfafi abin da zarar an fito da shi.

Shima Kabiru Isa manomine da ya halarci taron ya ce su dai sai sun gwada sun gani a zahir kafin su fara ammfani da sabuwar fasahar.

Ya ce zai ware gona guda a cikin gonakin sa idan sabon irin ya fito ya kuma gwada, idan ya bashi yadda ake fada to ko shakka babu zai rungumi fasahar ka’in da na’in.

Ko menen amfanin TELA maize

La’akari da cewa adadin al’ummar kasar nan ya kai miliyan 200, Najeriya na bukatar a kalla tan miliyan 20 na masara domin ciyar da al’ummar kasarta.

Ko da ya ke rahotanni sun bayyana cewa Najeriya ce kasar da ta fi kowacce noman masara a nahiyar Afrika.

Amma ko a shekarar 2019 Najeriya ta samar da tan miliyan 18 ne kawai, da hakan ke nuna har yanzu dai ba a iya noma masarar da za ta wadaci ‘yan kasa.

Hakan ta sanya dole kasar nan ke laruwa da shigo da masara da ga kasashen ketare domin cike gibin da ake shi.

Haka zalika masana na gani sai an shigo da kimiyya wajen magance matsalar karancin masarar da ake da shi a kasar nan.

Hakan ce ta sanya cibiyar (IAR) ta tsunduna bincike a bangaren kimiyyar sauya sarrafa halitta wato (Biotechnology)

Cibiyar ta yi nazari kwarai kan yadda za a samar da sabon irin da zai taimaka wajen magance matsalar karancin masarar.

A karshe dai ta fito da wannan sabuwar fasaha ta Tela maize, wani sabon irin masara da aka kirkira da zai jure karancin ruwa, ya kuma ya ki tsutsa, ya kuma samar da amfani mai yawa fiye da wanda aka saba gani.

Haka zalika cibiyar IAR a yanzu ta dukufa wajen ganin an samarwa da manoma wannan iri da zai taimaka wajen kawo karshen karancin masara a kasar nan.

Amfanin sa

Sabon irin zai taimaka wajen rage kudaden da manoma ke kashewa wajen noma masara.

Haka irin yana yabanya me kyau ko babu wadataccen ruwa a inda aka shuka.

Haka zalika irin yana yaki da duk wata tsutsa da ke cin masara, ma’ana ita wannan masarar tsutsa bata kamata.

Sanna sabon irin yana kara adadin kwayar masarar fiye da wace ake samu idan an yi shuka ba da irin ba.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending