KANUN LABARAI
An gurfanar da Rarara gaban kotu kan zargi rawa da matar aure

KANUN LABARAI
Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Aminu Abdullahi
Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.
Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.
Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.
“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.
“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.
Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.
Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.
Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

KANUN LABARAI
A harbe duk wanda aka gani da bindiga kirar AK47-Muhammadu Buhari

Mukhtar Yahya Usman
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin harbe duk wanda aka gani da wasu muggan makamai musamman ma bindiga kirar AK47 mutukar ba jami’in tsaro ba ne.
Kano Focus ta ruwaito cewar jami’in yada labaran shugaban kasar Malam Garba Sehu ne ya bayyana hakan ya yin da ya ke ztawa da sahsin hausa na BBC ranar Laraba.
Garaba Shehu ya ce shugaban kasar ya kuma bada umarnin a ragargaza dukkanin ‘yan ta’addan da suka ki su mika wuya.
Umarnin na shugaban kasa na zuwa ne jima kadan bayan da gwamnoni shida na yankin Arewa suka gudanar da wani taron yadda za su magance matsalar tsaro a jihohinsu.
Haka kuma gwamnonin sun bukaci fito da sabbin dabarun yaki da ga sojojin kasar nan domin dawo da zaman lafiya a yankunann da riki ya di-daita.

KANUN LABARAI
Ya zama dole a mayar da hankali kan bincikar kasafin kananan hukumomi-Kungiya

Aminu Abdulllahi
Wata kungiya mai suna Say No Campaign ta soki yadda al’umma ke mayar da hankalinsu kacokan kan gwamnatin tarayya kan al’amurn da suka shafi raya kasa.
Kano Focus ta ruwaito shugaban kungiyar Ezenwa Nwagwu ne ya bayyana haka yayin tattaunawa kan yadda al’umma za su bibiyi kasafin kudin kananan hukumomi a ranar Laraba a Kano.
Ya ce kananan hukumomi ma na yin kasafin kudi duk shekara, domim gudanar da ayyukansu, amma al’umma basu damu da bibiyar me suke yi ba.
“Suna maida hankali ne akan gwamnatin tarayya maimakon ayyukan da gwamnatocin su na jiha ko kannan hukumomi ya kamata suyi.
Bama sanya ido akan kananan hukumomi koda ace asusunsu a hade yake dana jihohi amma ana turo musu kudi da za su yiwa al’umma aiki.
“Kuma kudin da yake zuwar musu naku ne ba na aljihun su ba,” a cewar sa.
Ya kara da cewa rashin sanya ido akan kasafin kudin kananan hukumomi da al’umma ke yi yasa shugabannin ke karkatar da kudaden da aka ware don yin ayyuka.
Ya ce dokar ‘yancin samun bayanai ta 2011 ta kasa bata ta’allakaba ga kafafen yada labarai kawai.
Ya ce kowanne dan kasa yana da ikon neman bayani kan wani aiki da ya shafe shi daga gurin gwamnati.
Ya kuma ce matukar al’umma suka hada kansu tare da bibiyar yadda gwamnatoci da ke kusa da su suke kashe kudaden al’umma shakka babu za a samu raguwar cin hanci da rashawa.

-
KANUN LABARAI4 months ago
Budurwa ta kashe kanta a Kano ta hanyar rataya
-
KANUN LABARAI4 months ago
Gwamnatin Kano za ta mayar da ma’aikatan wasu hukumomin ta zuwa makarantu
-
KANUN LABARAI4 months ago
Yadda muka samu silin gashin manzan Allah a Kano-Sheik Karibullah
-
KANUN LABARAI4 months ago
Angwaye a Kano na daga aure saboda hauhawar farashin siminiti
-
KANUN LABARAI4 months ago
Zanga-zanga: yadda aka kashe yarana hudu a Kano.
-
KANUN LABARAI4 months ago
Jin waka na kara imani- Ibrahim Khalil
-
KANUN LABARAI4 months ago
Zanga-zanga: Ana zargin mutane hudu sun mutu a Kano
-
KANUN LABARAI4 months ago
Dalilai biyar da ya sa mata suka fi son namiji mai gemu