Connect with us

KANUN LABARAI

Ina hada baki ne da ‘yan unguwa su gayamin wanda ke da kayan da za a sata-Barawo

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Jami’an vigilante na unguwar Ja’o’ji a karamar Hukumar Kumbotso sun kama wani matashi da ake zargin ya kware wajen sace-sace a yankin.

Kano Focus ta ruwaito cewa barawon mai suna Abdul’alim Sani mazaunin unguwar Sheka ‘yar Kasuwa ya shiga hannun ‘yan sintirin ne bayan da ya haura wani gida a unguwar Ja’oji da karfe uku na daren ranar Talata.

Ya yin zantawar sa da jaridar Kano Focus  wanda ake zargin Abdul’alim Sani yace an kamashi ne ya yin da ya haura wani gida da tsakar dare inda ya kwashe musu wayoyi guda biyu da na’ura mai kwakwalwa.

Ya ce akwai abokanansa da suke ba shi bayanai na wadanda suke da mashin ko suka siyi sabuwar waya a unguwar wanda dasu ne yake gudanar da muguwar dabi’ar tashi.

“ Eh muna amfani da mukullin dake bude kowane abu kuma sunayen abokanan nawa akwai Hassan Kabila Da Tunbur da kuma Yazid Dadi kuma duk ‘yan nan unguwar ne.

“Kuma idan na sato wayoyin ina siyarwa da wani abokina ne mai suna Tamilo,” a cewar sa.

Ya kara da cewa ya siyar da kwmafutar da ya sato  a kan kudi naira dubu goma ga wani mai suna Abba Bari.

A nasa bangaren daya daga cikin wadanda barawon ya haurawa gida mai suna Alhaji Habibu Muhammad ya ce ya yi matukar farin ciki da ‘yan sinturin suka kama barawon.

Ya ce ba wannan ne karon farko da barawon yake yi masu sata ba dan kuwa ko akwanakin baya ma sai da ya haura ya dauke musu wayoyi da kayayyaki masu muhimmanci.

Sakataren kungiyar ‘yan sintiri ta unguwar Ja’oji Malam Musa Isah Murtala ya ce sun samu kira ne daga wani Alhaji Habibu Muhammad da karfe uku na dare inda ya shaida musu cewa wanda ake zargin ya haura masa gida.

Ya ce nan take suka garzaya gidan inda kuma sukayiwa barawon kofar rago tare da kamashi dumu-dumu da kayan da ya sata.

Ya kara da cewa barawon ya dade yana addabar unguwar ta Ja’oji kuma zasu miki shi zuga Hukumar yan sanda  don girbar abinda ya aikata.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending