Connect with us

KANUN LABARAI

Ko kun san mata dayawa a Kano basa wanka lokacin sanyi

Published

on

Share

 

Aminu Abdullahi

Wani bincike ya nuna yadda mata a Kano da ma saurarn sassan kasarnan ke kauracewa wanka lokacin sanyi.

A zantawar Kano Focus da wasu ‘yan mata a Kano sunce galibinsu kan kwashe kwanaki uku zuwa sati guda suna dakale a maimakon wanka.

Ko da yake al’umma na cewa lokacin sanyi lokaci ne da mata kan shiga takura ainun da hakan ke sanya su kauracewa wanka a lokuta da dama.

Amina Abubakar mai shekaru 23 da ke unguwar Na’ibawa a nan Kano ta sahidawa Kano Focus cewar da zarar lokacin sanyi ya yi , itakam ta yi sallama da wanka a kowacce rana.

Ta ce ta kan kwashe kwanaki uku a jere ba tare da wanka ba, sai dai ta dan wanke hannu da fuska ta kuma shafe su da mai.

A cewar ta da zarar sanyi ya yi tsanani to takan shafe mako guda ba tare da yin wanka ba.

“Kaga idan nayi kwaskwas dina shikenan koda fita zanyi danasa turare na shafa hoda babu mai gane cewa banyi wanka ba.

“Kuma ni abinda yasa bana wanka sosai saboda akwai sanyi kuma gaskiya zan iya kamuwa da cutar mura matukar nace zan dinga yi kullum,” a cewar ta.

Ita kuwa wata budurwa Hajara Abdullahi mai shekaru 24 da ke Unguwar Tunkuntawa ta ce maimakon wanka takan yi kwaskawarima ne da safe ta kuma mulke jikinta da mai.

Ta ce bayan kammala aikin yamma idan taga da faraga to sai ta yi wanka.

“Na kan yi wanka lokacin sanyi amma ba da safe ba sai bayan la’asar idan nayi girkin dare sai inyi wanka.

“Sai kuma da yamma ko washe gari zan sake wanka idan naga da hali.

“Amma idan zan fita unguwa nakanyi wanka da safe kamar bayan karfe goma.

“Idan kuma sammako zanyi barin wankan nakeyi saina dawo,” Inja Hajara.

Wata budurwar kuwa ‘yar shekaru 20, mai suna Rukayya Umar da ke Rijiyar Lemo ta ce tana yin wanka sau daya a sati ne kurum.

A cewar ta musamman idan ana sanyi mai tsanani  bata ga dalilin bata lokaci wurin yin wanka ba.

Ta ce yin wanka kullum a lokacin sanyi ganganci ne, domin yin hakan kan haddasa mata ciwuka daban daban musaman cutar  Nimoniya.

“Ko da yake ban fiye fita ba idan ba makaranta zanje ba, ko da naje makarantar ma a guri daya nake zaune, shiyasa bandamu nayi  wanka ba.”

“Yin wanka lokacin sanyi yana takura min sosai. inji ta.

Ita kwa wata budurwa Hafsat Sulaiman ta ce ba ta da tsari wajen yin wanka lokacin sanyi.

“Ni bani da tsari wajen yin wanka lokacin sanyi, nakanyi wanka ne kawai idan naga rana ta fito.

“Ba a ganin alama ko kadan idan banyi wanka ba saboda yanayin sanyi baya nunawa.” A cewar ta.

Ta ce kafin shigowar sanyi tanayin wanka akalla sau uku a rana amma ba yadda ta iya dole ta rage yin wanka saboda matsalar da yin hakan kullum zai jawo mata.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending