Connect with us

KANUN LABARAI

Rundunar ‘yan sandan Kano ta kama barayin zanga-zanga 59

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama mutane 59 da ake zargin suna da hannun kan tashin hankalin da ya faru a Kano yayin zanga-zangar #EndSARS.

Kano Focus ta ruwaito kakakin rundunar Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya sanar da hakan ya yin taron manema labarai da ya gudanar  ranar Laraba a shelkwatar rundunar da ke nan Kano.

Abdullahi Kiyawa mai mukamin mataimakin sufurtandan ‘yan sanda ya ce cikin mutane 59 da aka kama 31 ankamasu dumu-dumu da kayan jama’a da suka wawushe.

ya ce ko da ya ke an samu nasarar kwantar da tarzomar amma dai ‘yan tada kayar bayan sun kone babura 7, adai-daita sahu daya sai kuma motoci  biyu.

Haka kuma sun sace babura  8 suka kuma fasa shaguna 38 ciki har da babban shagon sayar da kayayyaki na Galaxy ta ke kan titin zuwa fili jirgin sama.

 

Wadanda ake zargin har ila yau sun sace kayayyaki a shagon sayar da abinci na Chicken Republic.

Haka kuma ya ce ragowar 28 din da aka kama dukkaninsu na da hannu kan tashin hankula da suka faru yayin zanga-zangar ta #EndSARS.

Ganima muka samu

Sai dai wasu daga cikin wadansa aka kama sunce su fa ba sata suka je yi ba gani ma ce suka dauka.

Yakubu Muhamamd Tudun Wada ya ce shi ko kadan bai  saci kayan kowa ba illa iya ka ganimar yaki ce ya gani ya kuma kwasa.

“Na dawo daga wurin aiki ne sai na tarar ana yaki tsakanin musulmi da   arna kuma naga ganima sai na kwasa.

“Donhaka ni ba barawo ba ne ban kuma saci kayan kowaba kuma ai ganima halak ce”. ya ce.

Shima Auwalu Musa da ke unguwar kwana hudu ya ce ko da ya ke an kamasu amma ba a kyauta ma sa ba domin shi kayan da ya dauka nag anima ne.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

KANUN LABARAI

Darakta Ashiru Nagoma ya samu lafiya

Published

on

Share

Mukhtar Yahya Usman

Fitaccen darktan shirya fina-finan Hausa Ashiru Nagoma ya fito daga Asibiti bayan da likitoci suka tabbatar da samun lafiyarsa.

Kano Focus ta ruwaito an sallamo shi daga asibitin ne da yammacin yau Alhamis.

Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga watan Janairu ne ‘yan uwansa da kuma kungiyar Fauziyya D Sulaiman suka kai shi asibiti, bayan anyi zarigin yana da tabun hankali.

Rahotannin sunyi nuni dacewa Nagoma ya shafe kimanin shekaru goma yana dauke da cutar tabin hankali.

Ko da yake al’umma da dama na ganin ba cutar tabin hankali ke damunsaba illa ta damuwa, ciki kuwa har da ‘yan uwansa.

Haka zalika makwanni shida ke nan kungiyar jin kai ta Fauziyya D Sulaiman da hadin gwiwar ‘yan uwansa suka garzaya dashi asibiti domin duba lafiyarsa.

Acewar dan uwa ga darktan Kabiru Abubakar Yusuf, Ashiru Nagoma ya samu lafiya sumul har ma an sallamoshi daga asibiti.

Kabiru Abubakar ya kuma mika godiyarsa ga dukkanin wadanda suka tallafa wajen samun lafiyar tasa, musamman Fauziyya D Sulaiman da kuma rukunnan Abokanansa Baki daya.

Haka zalika ya ce suna godewa duk wanda ya tallafa musu da addua wajen ganin dan uwan na su ya samu lafiya.

Continue Reading

KANUN LABARAI

NAFDAC ta kone jabun kayayyaki na milyan 600 a Kano

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Hukumar lura da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) to kone gurbatattun kayayyaki na sama da naira miliyan 600.

Kano Focus ta ruwaito cewa an gudanar da kone kayayyakin ne ranar Alhamis  a garin Hawan Kalewawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano .

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, daraktan hukumar shiyyar arewa maso yamma Dauda Gimba ya ce kayayyakin da aka kone sun hada da wandanda basu da rijista da kuma jabun kayayyaki da aka kamasu a jihar Kano da Kaduna.

Haka kuma wasunsu an an kama ne a jihohin Jigawa Katsina.

Sokoto da Zamfara sai jihar Kebbi.

Ya ce anyi hakanne don a tabbatar da cewa kayayyakin basu koma kasuwa ba don kar wasu su sake siyan su.

Ya kuma ce sun zabis u kone kayayyakin ne a jihar Kano sakamakon a nanne aka fi samun gurbatattun kayayyakin da ake siyarwa al’umma.

Ya ce al’umma su tabbatar da cewa duk abinda za su siya yana dauke da shaidair hukumar NAFDAC don gujewa yin amfani da abinda zai cutar da lafiyar su.

Continue Reading

KANUN LABARAI

Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali

Published

on

Share

Aminu Abdullahi

Shugaban majalisar malamai ta jihar Kano Malam Ibrahim Khalil ya ce za a tuhumi Abduljabbar Kabara ne kan abubuwan da yake furtawa amma ba mukabala za a yi da shi ba.

Kano Focus ta ruwaito cewa malamin ya bayyana hakane a ranar Alhamis ya yin da yake zantawa da manema labarai.

Ya ce za a zauna da shi ne a tuhume shi kan irin fatawoyin da yake bayarwa sabanin yadda mutane ke zaton cewa mukabala za ayi.

“Idan aka kira shi mukabala an canja masa ma’ana mutane suna cewa mukabala-mukabala, ba mukabala ba ce tuhuma ce.

“Tuhumar ita ce, ka ce abu kaza da kaza, to waye ya yi wannan bayanin a malamai, kamar yadda ka yi shi, a malamai na Musulunci waye kuma ya yi wannan fasarar da ka yi shi.

Ita kuwa mukabala ita ce kai kana cewa kaza wancan yana cewa kaza to sai a zo a zauna tsakanin naka da nasa wanne ne ya fi, shi ne za a yi mukabala, don a ga wanda nasa ne ya fi zama dai-dai,” a cewar sa.

Ya kara da cewa an dade ana kawo rigingimu daban-daban na fahimtar addini a jihar Kano amma ba a taba ganin irin fahimtar da Abduljabbar ya zo da ita ba.

Ya ce shi kansa mahaifinsa Malam Nasiru Kabara, bai taba hawa irin wannan turbar da ‘dan nasa ya hau ba.

Continue Reading

Trending